Thursday 23 December 2010

Shugabannin Afrika Na Karen Tsaye ga Democradiyya


Zabuka a nahiyar Afrika na neman zama wani abu daban. Abubuwan da yanzu haka ke faruwa a kasar Cote d’Ivoire abubuwa ne da ke tayar da hankali ga duk wani mai san ganin ci gaba a nahiyar Afrika, abubuwa ne dake tayar da hankali ga ma’abota tsarin mulki irin na democradiyya.

Bayan shafe shekaru 10 yana mulki a kasar ta yammacin Afrika, da kyar da jibin goshi Laurent Gabgbo ya amince ya gudanar da zaben kasa baki daya. Dama dai kada mu manta cewa kasar ta yi fama da yaki da tashe-tashen hankula, lamarin da sai da kasashen duniya da majalisar dinkin duniya suka yi wurjanjan kafin su kawo karshen sa.

A watan jiya an yi zabe. Kuma ‘yar manuniya ta nuna. Abunda kuwa ta nuna shine cewa Alhassan Ouattara ne ya lashe zaben. Amma sai me zai faru?

Sai shugaban da ya shirya zaben Laurent Gabgbo yayi kememe ya ce ba zai sauka daga mukami ba, bayan kuwa hukumar zaben kasar mai zaman kanta ta bayyana sakamakon da ya nuna Alhassan Ouattara ne ya yi nasara.

Laurent Gabgbo ya rantsar da kansa a matsayin zababben shugaban kasa. Shima kuma Alhassan Ouattara ya bayyana kansa a matsayin sabon shugaban kasar ta Cote d’Ivoire.

Kasashen duniya sun yi Allah wadai da karan-tsayen na Mr Gagbo, kuma kawo yanzu tuni har an fara zub da jini, abunda kuma Allah kadai ne ya san inda lamarin zai tsaya.

Babban abunda lamarin na Cote d’Ivoire ke nunawa shine shugabannin Afrika basu san menene democradiyay ba. Basu yadda cewa jama’a zasu iya sauya shugabanninsu ta hanyar dangwala dan-yatsa bisa katin zabe ba.

Yana kuma nuna cewa shugabannin Afrika ‘yan kama-karya ne, wadanda ba sa mutunta bukatun jama’arsu. Dama a ce ma suna yiwa kasa aiki ne, suna kawo kyakkyawan ci gaba ga rayuwar talakawa, to dama da sauki. To amma mulki a nahiyar abune na “ramin-kura”.

Kada kowa ya raba daya biyu cewa abunda ya faru a Cote d’Ivoire ba zai iya faruwa a sauran kasashen Afrika ba. Ko shakka babu hakan zai iya faruwa a kowacce kasa a nahiyar; domin kuwa launin shugabannin – abunda Hausawa ke cewa ne – duka kanwar ja ce.

Sai dai manyan tambayoyi su ne: har ya zuwa yaushe ne jama’ar Afrika, da talakawa zasu ci gaba da amincewa da mulkin kama-karya? Har zuwa yaushe ne shugabanni za su ci gaba da taka bayin Allah saboda suna takama da karfin iko da kujerar da suke kai?

Mai yiwuwa talaka ba zai iya ba, kodai saboda tsoro, ko saboda rashin sanin ‘yancin kansa. Sai dai idan su ba zasu iya ba, Allah zai iya musu.

A karshe ina mai tsinkayen wani lokaci a gaba, da idan ance shugaba yayi irin abunda ke wakana a Cote d’Ivoire yanzu, zai ranta a na kare, ya ce “ku rufa mani asiri”.

Allah ya nuna mana wannan lokaci ko mulkin adalci da gaskiya ya wanzu a nahiyar mu. Allah ya kawo mana karshen karen-tsayen da shugabanni ke yiwa tsarin democradiyya a Afrika.

Wednesday 15 September 2010

Kashe-Kashen Gilla a Nigeria: Yaya Za Mu Yi da Ranmu?


Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Wannan tashin hankali da ake ciki a Nigeria, ubangiji Allah Ka yi mana maganin sa. A matsayin mu na ma’aikatan aikin watsa labarai, wannan makon ya kasance maras dadi. Maras dadi, saboda rahotannin kashe-kashe da daukar rai a kasar da muka fi maida hankali akanta a aikin na mu, wato Nigeria.

Ranar litinin a cikin shirin BBC Hausa na rana Yusuf Ibrahim Yakasai ya kawo wani rahoto wanda a cikinsa yake cewa an hallaka wasu mutane biyar, 'yan gida daya, a cikin daren lahadi. Wasu mutane ne da ba a shaida ko su wanene ba, suka shiga wani gida, a rukunin gidajen dake unguwar Kundila dake kan titin Gidan Zoo, a birnin Kano, suka yanka magidancin mai suna Garba Bello, mai kimanin shekaru hamsin da biyar, tare da matarsa, da kuma 'ya'yansa ukku.

Mun ji yadda yayar matar gidan da aka yanka, tana bada labarin yadda ‘yar-uwar ta da aka yanka din ta buga mata waya tana neman dauki. Amma kuma suna cikin magana sai wayar ta katse. Abunda yasa take jin a wannan lokacin ne maharan suka farma ‘yar uwar ta ta.

Ana cikin wannan jimamin kuma, a ranar talata sai muka ji Nurah Ringim yana hira da wata mata tana kuka, tana shash-sheka, tana maida yadda wasu mutane da ba’a san ko su wanene ba, suka shiga gidan su, suka harbe mai gidanta har lahira.

Marigayi Malam Abdullahi Muazu dai babban jami'in hukumar EFCC, mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa ne. Hukumar EFCC ta danganta kisan nasa da hare-haren da tace ana kaiwa jami'anta a halin yanzu.

Ana cikin yin haka sai Abba Katsina ya aiko mana da rahotan wani lamari da ba’a saba gani ba a arewacin Nigeria, inda wani matashi dan shekaru ashirin da biyu, ya kashe kansa da kansa. Matashin mai suna Murtala Ibrahim - wanda aka ce makarancin Al-Kur'ani ne - ya kashe kan nasa ne ta hanyar ratayewa. An tsinci wata takarda kusa da gawar tasa, inda ya rubuta cewa, ya kashe kan nasa ne, domin ya kawo karshen zaman da yake yi na rashin aikin yi.

Ko shakka babu, wadannan labarai masu ta da hankali ne ga duk mai hankali. Domin kuwa suna nuni da mummunan halin da aka shiga a kasar mu Nigeria. Mummunan hali ta kowanne fanni: fannin tsaro, fannin imani, fannin hankali da dai sauransu.

Yanzu haka babu wani mahaluki a Nigeria da zai iya cewa ya shige a afka masa, a hallaka shi ko wani nasa. Jama’a suna cikin matsananciyar fargaba.

A kasashen da suka ci gaba hukumomi da jami’an tsaro suna kare rayukan jama’a. Amma a Nigeria, harin ma harda su jami’an tsaron ake kaiwa baya ga jama’ar gari.

Tambaya anan shine, wai me ya kawo wannan halin lahaula da Nigeria take ciki? Laifin wanene? Yaushe ne ‘yan Nigeria zasu samu fita daga cikin masifar da suke ciki a kasar su?

BBC Hausa zata tattauna wannan batu a shirin “Ra’ayi Riga” na wannan makon. Sai ku kasance da BBC Hausa.
http://www.bbc.co.uk/hausa/

Monday 23 August 2010

Wasu na Shan Ruwan Bunu a Watan Azumi, Wasu na Shan Kindirmon Kwali


Watan Azumi wata ne mai alfarma ga dukkanin Musulmi a koina a cikin duniya. Kuma yau, a kwana a tashi, gashi har wata yana neman rabawa. A duk tsahon wannan watan BBC Hausa tana kawo rahotanni da sakonnin “shan ruwa daga masu sauraron mu”.

Wasu sun aiko mana da tambaya suna cewa mecece fa’ida ko hikimar kawo sakonnin “shan ruwa daga masu sauraron mu?” To lallai ga wanda bai kalli lamarin cikin zurfin tunani ba zai ga tamkar ba wani abu ba ne illa kawai kawo mutane suna cewa sun ci kaza sun sha kaza. A saboda haka kenan wannan ba abu ne mai mahimmanci ba.

Sai dai ni kuwa ba haka nake kallon abun ba. Ina kallon sa ne daga fannin launin abincin da mafi yawan jama’ar mu ke ci a wannan wata mai tsarki bayan sun kamalla ibadar su da magariba.

Kowa dai ya wuni da azumi, zai so ya yi buda baki da dan abun marmari da kuma ababen gina jiki wadanda zasu mayar da gurbin abunda aka rasa a yayin azumin. Sai dai sauraron irin abunda da mafi yawan al’ummar Hausawa ke shan ruwa da su, abu ne dake kawo hawaye a ido.

“Ni dai yau na sha ruwa da ruwan bunu da rama; yau na ci dabino da kunun kanwa, illa iyaka; ni dai na sha ruwa da dan-wake da mai da yaji, iyakar abunda Allah ya hore min kenan, Allah ya nuna mana gobe lafiya!”

Wadannan sune kadan daga dubban sakonnin da BBC Hausa ke samu a kowanne dare. Me sakonnin suke nuna mana? Lallai suna yin nuni ne da irin wahalar da jama’a suke ciki a kasar mu. Kuma yayinda miliyoyi ke shan “ruwan bunu” wasu ‘yan tsiraru kuwa suna shan kindirmon kwali mai sanyi da naman kaji.

Nigeria dai ba kasa ce matalauciya ba. Amma kuma jam’a na cikin halin matanancin talauci. An san dalilan da suke janyo talaucin: rashin shugabanci na-gari, rashawa, almundahana, rashin adalci da tsananin san-kai. Kididdgar Majalisar Dinkin Duniya na cewa mafi yawan ‘yan Nigeria na rayuwa ne akan kasa da Dala daya – wato kasa da Naira 150 - a rana.

A wannan lokaci na ibada kamata yayi mu kara tunani a game da halayyar mu ko Allah zai ji tausayin mu. Mu gyara halayen mu sannan kuma mu roke Shi Ya ba mu shugabanni masu tausayin talakawa, wadanda zasu fitar da al’ummar mu daga kangin talauci.

A sha ruwa lafiya!

Tuesday 29 June 2010

Talauci na Janyo Mutuwar Mata Wajen Haihuwa


Da alama matsalar mutuwar mata sanadiyyar haihuwa, na ci gaba da ci wa al'ummar yankin arewacin Nigeria tuwo a kwarya. Kodayake dai wannan ba matsala ce da ta addabi kasar Nigeria kawai ba, a'a sauran kasashe masu tasowa musamman ma a nahiyar Africa su ma suna dimbin hasarar rayukan mata da jira-jirai. Alkaluman hukumar UNICEF na nuna mace daya daga cikin goma sha-uku na mata masu juna biyu kan rasa rayukan su a lokacin haihuwa a nahiyar Afrika.

A wani rahoton BBC, wakilin jihar Jigawa, Muhammad Annur Muhammad, ya bayyana cewa a shekaru ukun da suka shige, alkaluma sun nuna cewa jihar Jigawan ce kan gaba a Nigeria a wannan matsala.

A jihar Borno ma, mata na rasa rayukan su a kullum idan suka zo haihuwa. Duk da bayanan da suke nuna cewa an soma samun nasarar rage matsalar a wasu kasashen tun bayan rattaba hannun kan kudurorin Muradan Majalisar Dinkin Duniya na shekara ta 2015 da shuwagabannin kasashe 147 suka yi, har yanzu akwai jan aiki a gaban Bornon. Lamarin haka yake ma a sauran jihohin arewacin Nigeria. Kodayake dai an tabbatar da cewa shiyyar arewa maso gabashin Najeriyar ce da har yanzu alkaluma ke nuna matsalar tafi ta'azzara.

Amma kuma wasu jihohin arewacin Nigeriar na dan tabusawa. A jihar Jigawa, Mohammed Annur Mohammed na BBC Hausa, ya ce gwamnatin jihar ta shigo da wani shiri wanda ya kunshi horar da al'ummomi musamman na yankunan karkara su kafa wata kungiya da hukumomin ke ilmantar da su bisa hanyoyin kula da mata masu juna biyu, tare da ba su motoci don hanzarta kai matan asibiti.

Akwai matsaloli daban-daban dake janyo mutuwar mata masu juna biyu idan suka zo haihuwa. Babbar matsala dai ita ce talauci. Matan talakawa masu juna biyu sun fi yiwuwar mutuwa idan aka kwatanta da matan mazaje masu hannu da shuni. Saboda rashi, matan talakawa ba sa samun abinci mai gina jiki.

Baya ga wannan, sukan yi ayyuka na karfi, da wahala kamar su noma da surfe da sussuka, har zuwa lokacin da suke gab da zuwa kan-gwiwa. Karfin su kan kare a lokacin da haihuwar ta zo, wanda kuma a lokacin ne suka fi bukatar karfin.

Haka kuma mata marasa ilimi sun fi yiwuwar rasuwa wajen haihuwa fiye da mata masu ilimi saboda sun fi su sanin hanyoyin kaucewa daga wasu haddura; kana sun fi su sanin mahimmancin zuwa asibiti - tun daga lokacin awan ciki har ya zuwa lokacin haihuwa. Alal misali kididdiga ta nuna mata masu ciki biyu cikin goma ne kawai ke zuwa asibiti a jihar Jigawa a yayin da suke da juna biyu.

Matan dake zaune a kauyuka sun fi yiwuwar rasuwa a wajen haihuwa fiye da matan dake zaune a birane. Rashin asibitoci a kauyuka ko kuma nisan da suka yi daga birane na nufin mata masu juna biyu basu cika samun kulawa cikin hanzari a lokacin da suke nakuda ba. So tari kan a je asibiti, sai ka ga rai yayi halin sa. So tari ma har da na jaririn.

Muddin dai yankin Arewacin Nigeria na san cimma manufofin raya kasa, bunkasa da tattalin al'ummar su, ya zama wajibi su tashi haikan wajen tabbatar da daukar matakan da zasu magance wannan matsalar dake janyo hasara mai dimbin yawa ga yankin. Saka idanu wajen kula da jama'a, musamman talakawa babban hakki ne da ya kamata su sauke.

Wednesday 23 June 2010

Dambe a Majalisar Nigeria: Halin Dattaku?



Hoton dan majalisar wakilan Nigeria kenan Dino Melaye, shugaban kwamitin “Progressive Forum” masu fafutukar kawo sauyi a majalisar wakilan Nigeria. Hotan na nuni da yadda taguwar da yake sanye da ita, ta yage, kana gashi yana sharba gumi. An dai dauki hoton wannan dan majalisar ne bayan damben da aka sha a majalisar wakilan Nigeriar.

Majalisa ta nemi a fitar da ‘yan kungiyar “Progressives” din ne da karfin tuwo bayan sun nemi da a binciki shugaban majalisar wakilan Dimeji Bankole a bisa zargin sama da fadi da kudin jama’a da mulkin kama-karya. Wasu ‘yan majalisar sun fito shabe-shabe yayinda shi kuwa dan majalisa Chinyere Igwe ya samu karaya a hannu bayan wani dan majalisar ya kai masa hari da tukunyar iskar kashe gobara.

Rikici a majalisar dai ya barke ne a jiya (22/06/10) bayan da jim kadan bayan majalisar ta fara zaman ta, kakakinta Bankole ya nemi wani dan majalisa da ya gabatar da moshan (kuduri).

Amma da Mr Melaye ya dago cewa ana kokarin gabatar da moshan din da zai dakatar da ‘yan Progressives” din daga majalisa, sai ya mike, ya fara ihu, yana cewa, “ babu hali, babu hali, ba zamu yadda ba”, yana kuma busa wani usur da ya shiga da shi cikin majalisar.

Kafin a ankara sai wuri ya yamutse, sai naushin juna. An dai yi wannan lamarin ne a gaban ‘yan jarida wadanda kuma suka dauki hotuna da bidiyo. Nan take kuma wasu ‘yan majalisar da jami’an tsaro suka yi kokarin kwace hotunan da ‘yan jarida suka dauka saboda kada duniya ta ga abun kunyar da shugabannin jama’ar suka aikata.

Tuni dai jama’a a ciki da wajen Nigeria suke ta bayyana ra’ayinsu dangane da halayyar mutanen da aka dorawa alhakin yin doka a Nigeria.

A tsakanin kowacce al’umma dake da nutsuwa da sanin ya kamata dai akwai wasu halayya da dabi’u da ya kamata manya su nuna. Mutunta juna, musamman wajen tunkarar mai da martani ga ra’ayin da ya banbanta da na wani na ga kan gaba.

Tsarin democradiyya kuma na jaddada mahimmancin muhawara da bayyana ra’ayi, amma cikin hankali da kwanciyar hankali ba ta hanyar zagi-in-zaga da doke-doke ba.

Dambe da baiwa hammata iska da amfani da makami dan jikkata wani, baya daga cikin halayya ko dabi’un da ake alakantawa da zababbun wakilai masu yiwa kasa doka. Idan kuwa suka yi hakan, lamarin ya kasance mai dokar barci ya bige da gyangyadi kenan. Kuma wabiji ne a hukunta su domin hana faruwar hakan a gaba. Babba, ai misali mai kyau ya kamata ya nunawa na kasa!

Masu sharhi na cewa damben da ya faru a majalisar wakilan Nigeria abun takaici ne. Kuma a cewar su, na nuni da rashin sanin ya kamata da karya mutuncin tsarin democradiyya a Nigeria. Wasu suka ce a daidai wannan lokaci da Nigeria ke kokarin gyara martabar ta a idanun duniya “re-branding”, sai ga manyan jami’an tsarin democradiyya kasar suna kokawa da juna. Tuni dai hotunan wannan abun kunya suka mamaye yanar gizo “internet” inda miliyoyin jama’a suke ta dubawa suna sharhi.

Daga cikin tambayoyin da ake yi yanzu haka har da: shin ‘yan majalisar Nigeriar suna dambe da juna ne saboda kare hakkokin jama’ar da suke wakilta, wadanda kuma talauci da matsayin rayuwa ya addaba, ko kuwa suna baiwa hammata iske ne bisa wasu bukatu na su na kashin kansu?

Sashen Hausa na BBC zai duba wannan batu a wannan makon a shirin sa na “Ra’ayi Riga”.

Wednesday 28 April 2010

Matasa da Bangar Siyasa a Nigeria


Yanzu haka an fara shiga yanayin siyasa a Nigeria wato yayinda ake shirin gudanar da zabukan shekara mai zuwa.

Siyasa na da mahimmanci a kowacce kasa ta duniya dake bin tarafkin democradiyya. Dalili kuwa shine siyasar tsarin democradiyya na baiwa jama’a damar zabar wanda suke ganin ya dace da su, kuma wanda zai biya masu bukatun su da kuma share masu hawaye.

Jama’a kan ba da goyon baya ga wanda suka yi imanin zai wakilce su – kuma wakilci na gari – ba wanda zai je dan wakiltar kan sa ba. Ta yaya jama’a ya kamata su tabbatar da cewa sun zabi na gari ba zaben tumun dare ba?

Mai yiwuwa sai nan gaba zamu tattauna wannan batu. Amma ina so na yi a wannan sharhi ne akan siyasar banga.

Tun bayan da Nigeria ta koma tsarin democradiyya yau shekaru sama da goma ‘yan siyasar kasar ke amfani da matasa domin cimma manufofin su na siyasa. Ba laifi ba ne ‘yan siyasa su nemi goyon bayan matasa. Misali a baya-bayan nan, kuri’a da goyon bayan matasan Amruka ta taimaka gaya wajen nasarar shugaba Barack Obama a 2008.

Abunda yake laifi shine amfani da matasa a matsayin ‘yan bangar siyasa domin samun nasara a zabe. A zabukan da suka wakana a baya ‘yan siyasa a Nigeria na baiwa matasa kudi, inda su kuma sukan sayi kwaya da sauran ababen sa maye da makamai, suna bi suna razana abokan hamayya da sauran jama’a.

Kamar yadda na gani a wannan hoto dake kan wannan shafi (wanda na dauka sa’ilin da na kai ziyara Bauci a watan jiya), rikici kan rincabe tsakanin ‘yan bangar siyasa. Akan yi fito-na-fito tsakanin ‘yan bangar ‘yan siyasar. Wani lokaci a ji munanan raunuka, a wasu lokuta a rasa rayuka. Wannan abun takaici ne.

Shin matasan nan da suke bari ana amfani da su dan cimma manufar zabe, duk da cewa sun san ‘yan siyasa zasu yi watsi da su, da zarar sun yi nasara, sun san ciwon kan su kuwa? Suna da masaniya kan cewa ‘yan siyasa basu damu da su ba illa kawai sun mai da su tamkar matattakala ce da suke takawa domin “cin zabe” ko ta halin kaka?

Amsar da nake san sani itace: ta yaya ne matasa zasu jajirce su ki yarda ana amfani da su a matsayin ‘yan bangar siyasa a bisa kudi kalilan – wadanda akewa kallon marasa mutunci a Nigeria - lamarin da ka iya sanadiyyar hasarar rayukan su da ci bayan kasar su?

Sunday 4 April 2010

Facebook | Yaushe Za Su Gane?

Jiki Magayi - Talaka na Mutuwa a Rikice-Rikice


Rikicin addini da na siyasa sune manyan labarun dake janyo fargaba ga Edita ko shugaban kafar yada labarai. Alal misali wajibi ne na tabbatar da cewa mun bada labarin rikice-rikicen addini da kabilancin ba tare da nuna san zuciya ga kowanne bangare ba. Haka ma rikicin siyasa.

Babban abunda na lura da shi a aikina shine a Nigeria kusan kashi casa’in cikin dari na rikice-rikicen da ake yi, manya ne suke ta da su. Manya sun hada da wasu masu kudi, da wasu malaman addini na Musulunci ko Kirista, da wasu ‘yan siyasa.

Tun lokacin da Nigeria ta kama bin hanyar democradiyya a 1999, kasar ta yi fama da rikice-rikicen addini da kabilanci daban daban. Tun daga rikicin OPC Shagamu, Kano, Zangon Kataf, Tibi, Yalwan Shandam har zuwa na baya-bayan nan, wato su Boko Haram, Kala Kato da kuma rikice-rikicen Jos.

Masu bincike sun yi ittifakin cewa manya na da hannu a wadannan rikice-rikice. Suka ce wannan ne ma ya sa aka ki hukunta kowa.

A hirar da na yi da shi a BBC Hausa, tsohon sarkin Gwandu Alhaji Mustapha Jakolo ya yi tambaya mai mahimmanci. Ya ce “kin taba jin wani babban mutum, ko shugaban addini na Musulmi ko na Kirista da aka kashe, ko kuwa ‘ya’yan su? A kullum aka tashi masifa a Nigeria, hasara na tsayawa ne ga talakawan kasar.”

Wannan maganar haka take. Da na je Jos a kwanannan, ilahirin hasara – ta rai da dukiya – ta kare ne kan talaka. Wannan ne ma ya sa ni tambayar: me yasa talakawa ba zasu gano cewa wasu na amfani da su ba ne domin cimma wata manufa? Wani da wahala, wani da riba – shine abunda ke faruwa.

Abunda zan so in ji daga gareku shine: yaushe ne talakan Nigeria zai koyi darasi? Yaushe ne zai daina yarda wasu manya suna amfani da shi, kuma a karshe hasara rai ko ta dan abunda suka mallaka ta komo kansu? Yaushe zai ce, “idan kana so muyi kashe-kashe bamu ‘ya’yan ka mu je tare”?

Lokaci yayi da talaka zai jajirce ya ki karbar ‘yan tsirarun Nairori dan biyan bukatar wasu da a zahiri basu damu da su ba, domin iyalan su na turai su na karatu ko shakatawa da kudaden da ake zargin sun kwashe na su talakawan.

Hausawa dai suka ce jiki magayi.

Saturday 27 March 2010

Facebook | Tilin Shara a...

Facebook | Tilin Shara a...

Tilin Shara a Biranen Mu


Ban sani ba ko wani zai gane wannan tilin sharar dake wannan hotan. To wannan dai wata unguwa ce a birnin da yafi kowanne girma a nahiyar Afrika. Wato birnin da na fito, birnin da aka haife, Kano.

Kusan ta kowanne bangare Kano shine birnin da ya fi kowanne birni a Nigeria. Wannan ma shi ya sa ake masa kirari da: Kano, ko da mai ka zo an fika. Sai dai kuma tsakani da Allah, ba komai ne ya kamata a ce birni na, yafi saura akai ba.

Ba alfahari ba ne a ce birni na shi ya fi kowanne kazanta ko tarin shara a Nigeria ko Afrika. Idan na zo da baki ina yawo da su a garin nakan ji matukar kunya. A gaskiya ma, akwai unguwannin da bana bi da su.

Na yadda kan cewa yawan jama’a na taimakawa wajen taruwar shara a kankanin lokaci. To amma musun da nake san yi anan shine, ai idan aka samar da wata hanya kyak-kyawa, mai tsari, ta kwasar shara akan kari, ba tare da bata lokaci ba, to kuwa za’a rage afkuwar matsalar tarin shara a Kano.

A lokacin da nake korafin tilin shara a garin mu, sai na tuna cewa a gaskiya matsalar tarin shara a tsakiyar al’umma ba matsala ce da ta tsaya a Kano kawai ba. A’a!

Kusan ilahirin biranen arewacin Niigeriar da na je a shekarun nan na fama da matsalar shara. Sai dai a ce wasu sun fi wasu.

Tilin shara a tsakiyar al’umma na kawo barazana kala’kala ga bil adama. Alal misali saboda dankarewar sharar da ta hada da tsummokara, leda, bawawwaki, dusa, kashin awaki, takardu, kai da duk wani abu maras amfani, wadanda akan jigba akan magudanan ruwa, sauro ke cin karen sa ba babbaka. Sakamakon wannan kuwa itace cutar cizon sauro wato Malaria a turance.

Abun da kan bani mamaki kuma shine yadda zaka ga masu suyar kifi ko balangu sun soye-soye ko gashe-gashen su a dab da tilin sharar. Kuma mutane suna ta siya ba tare da tunani hakan na iya janyo musu cuttukar kamar su amai da zawo da Thypoid ba.

Haka kuma sai ka ga yara da matasa suna tsince-tsincen robobi ko rafta – kamar yadda ake cewa a Kanon – dan siyarwa.

Idan hukuma na da laifi, suma jama’ar unguwa da gari suna da nasu laifin. Menene ya sa ba za’a hada kai, a fitar da wani tsari da zai tabbatar da jama’a ba sa zubar da shara a ko ina ba sai inda hukuma ta shata? Me yasa mutane basu damu da kiwon lafiya da tsaftar muhallin su ba?

Mai yiwuwa wasu su ce ai matsalar shara kadan ce, akwai wadanda suka fi ta girma. Amma a nawa tunanin wannan ma matsala ce musamman tun da tana barazana ga lafiyar al’umma.

Me ya kamata mu yi akan matsalar shara a biranen mu? Zan so in ji daga duk mai shawara.

Sunday 21 March 2010

Ana Ga Yaki Suna Ga Kura


Babu shakka kasashe masu tasowa na fama da dimbim matsaloli. Mafi yawan wadannan matsaloli kuma mutane ne ke janyo su – ba wai Allah ne ke doro su ba. Kodayake dai kusan a kowanne lokaci mu kan danganta abubuwan mu ga kaddara, amma kuma wajibi mu kasance masu taya Allah kiwo.

Ina Kano a ranar da gobarar ta tashi a kasuwar kantin Kwari. Na isa kantin Kwarin bayan da mai aikowa da BBC rahotanni daga Kano, Yusuf Ibrahim Yakasai ya bugo mani waya jim kadan bayan misalin shida da rabi na safiya.

Koda na isa kantin Kwari sai na iske dubban mutane sun yi cincirundo, ana ta firmitsi-mitsi. Na ga wadanda nake zaton ‘yan kasuwa ne suna kici-kicin kwashe kayan su daga shagunan dake kusa da wadanda ke cin wuta – musamman ma dai gidan Labaran wanda a wannan lokaci yake ta ci da wuta.

Baya ga masu kokarin kwashe kaya, sai kuma ga ‘yan kallo. Wadannan sune mutanen da suka ba ni mamaki. Su wadannan mutane samari da manya, sun je wajen gobarar ne wai dan kashe kwarkwatar idanu. Yawan ‘yan kallon ya sanya an samu cunkoso a bisa ‘yar siririyar hanyar da ita ce masu motar kashe gobara za su bi.

‘Yan kallon ba su yi tunanin cewa gobara ba abar kallo ba ce, da kuma cewa suna saka rayuwar su da lafiyar su a cikin hadari. A yadda na ga ginin ke ci da wuta, kiris yake jira ya ruguzo kasa. Ina cikin wannan tunani sai na ji ana “ku gafara, ku gafara, ginin zai fadi”.

Sai rududu...jama’a suka fara gudu. Allah dai ya kiyaye firmitsi-mitsin bai kai ga jikkata ko hallakar kowa ba.

Wani abu da na lura da shi a lamarin gobarar kantin Kwarin kuma shi ne aikin tsarin ceto idan wata masifa ta auku a Nigeria. Ni dai har na bar wajen, motar kashe gobara kwaya daya kacal na gani (kamar yadda wannan hoto ya nuna). Kuma ban ga ta na feshin ruwa a lokacin da naje ba. Da na yi tambaya sai aka ce wai babu ruwa amma ana jira za’a kawo.

Bayan wani lokaci na bar wajen. An dai ce ruwa ya samu isa, kuma an samu kashe gobarar da ta fara ci tun karfe daya na safe har zuwa misalin bayan azahar – wato wajen sa’o’i 12-14 kenan. Ganin tsukukun wajen, Allah ne kawai ya takaita ta’adi da hasara.

Idan akwai masu lissafin gobarar kantin Kwarin da ta faru a wannan watan, to wajibi ne su yi nazari kan batutuwa da dama da nufin daukar darussa domin kiyaye gaba. Kadan daga wadannan su ne:

Ya kamata kayayyakin ceto da agaji kamar na kashe gobara su kasance a kowacce kasuwa ta yadda ba sai gobara ta tashi ba za’a shiga nemo mota da ruwan kashe ta?

Shin ginin kasuwannin mu ne irin na zamani ne ta yadda zasu kasance an samu raguwar masifu kamar gobara da ambaliyar ruwa?

Akwai hanyoyi masu fadi da za’a iya kaiwa ga kantina ba tare da masu aikin agaji ko ceto sun samu matsala ba?

Ya kamata jami’an tsaro kamar su ‘yan sanda su shiga aikin killace wajen da matsalar ta afku saboda hana ‘yan kallo cushe wajen?

Shin akwai wata hanya da za’a ragewa wadanda irin wannan masifa ta afkawa radadi wato ta hanyar basu tallafi? Domin kuwa a ganina idan ba wani ikon Allah ba, gobarar nan ta kantin Kwari zata kasance karshen wasu kenan.

Mai yiwuwa idan muka tunkari wadannan batutuwa mu taya Allah kiwo.

Allah ya kiyaye.

Monday 1 March 2010

Komai da Ruwanka


Bayani abune mai matukar mahimmanci ga kowanne dan Adam, ga kowacce al’umma, kuma ga kowacce kasa. Ingancin bayani kan baiwa mutum damar daukan matakai ko matsayar da suka dace a gareshi – abunda a turance ake kira “informed decision”. Misali idan baka da bayani akan abu, kana aka zo aka yi maka tambaya akan abunnan, to shaci fadi za ka yi, ko gaibu, ko kuma ka fadi abunda ba gaskiya ba.

Aikin ‘yan jarida shine nemo labarai komai dacin sa, sannan ka fada ba sani, ba sabo. Aikin jarida yana da ka’idoji da sharruda kamar kusan kowanne aikin kwararru. Alal misali BBC, kamfanin jaridar da ya fi kowanne suna a duniya, ya ginu akan wasu ginshikai: gaskiya, tsayawa a tsakiya wato babu goyon bayan wani bangare da kuma adalci –wato baiwa kowa hakkin sa. Watakila saboda tsayawa kan wannan manufa ta aikin jarida ne ya sa BBC ta yi fice a aikin jarida a duniya.

Tarihi ya nuna cewa a da, BBC ta kan dauki ma’aikatan da lallai ba ne a ce suna da takardar shaidar digiri. Amma yanzu saboda akwai gasa ta kowanne fanni har ma da a fannin aikin jarida, ya sa gidajen jarida kamar su BBC din neman wadanda ke da wani adadi na ilimi kafin a dauke aiki. Aikin jarida a duniya irin ta yanzu, wato mai saurin sauyi saboda ci gaba ta fannin fusaha, ya sa ana matukar bukatar gogewa muddin dai za’a ci gaba da kasancewa a gaban wadanda ake gasa da su a fagen aikin jaridar.

Ban san abunda ya yi tunani akai ba amma Malam Bashir Sule Kofar Sauri dan dandalin zumunta na BBC Hausa Facebook ya aiko mani sako kamar haka: “Hajiya ina da tambaya game da wannan profession din naku, wai yaya, ko sakandare mutum ya gama in dai ya shiga aikin jarida sai ya dunga kiran kan shi journalist. Ba wani matsayi da mutum sai yakai kafin ya kira kanshi journalist, koko yaya ne?

Na aikewa da Bashir, amsa inda na ce, “Haka yake a (wasu kasashe ciki har da) Nigeria mutanen da basu cancanci yin wani aikin ba, sai ka ga suna yi. Ga misali: kana bukatar takardar shaidar kammala karatu na musamman kafin ka fara harhadawa da siyar da magunguna. Amma a Nigeria kowa zai iya siyar da magani - har a tire mutane suke dauka, suna yawo da shi a ka. Kai dai kawai sai dai mu roki Allah ya yaye mana halin da muke ciki a kasar mu”.

Malam Bashir ya sake mai da mani da martani inda ya ce “haka yake sunan su doctors haka ma ake kiran su a Lagos. In ba ka ce doctor da karfi ba ma, ba zai juyo ba”.

To wannan matsala dai akwai ta a aikin jarida. Da akwai wadanda ba su da wata cikakkiyar shaidar karatu, amma su na aikin jarida. Har kamfanin jarida ma suke budewa. Ba wai ina cewa sai karatun ka ya kasance a fannin jarida ba, a’a. Za ka iya aikin jarida idan kana da digiri a wani fanni da ba aikin jarida ba amma kuma sai ka yi ta kwasa-kwasai daga kwararrun kamfanonin aikin jarida har ka zama gogaggen dan jarida. Alal misali BBC ba ta dagewa kan cewa sai kana da digiri a aikin jarida kafin a dauke ka aiki; amma kuma lallai sai mutum ya kasance yana da digiri.Da zarar ka zo BBC, za’a baka horaswa abunda kuma har ka bar gidan, ba za ka daina yi ba. A shekaru kusan 18 din da na yi ina aiki da BBC, na yi kwasa-kwasai da suka haura 40 – tun daga kwas na sa’o’i, zuwa na makonni. Hatta ma a makon jiya sai da nayi na rabin wuni.

Tambayar da Malam Bashir Kofar Sauri ya yi mani ta sa ni tunani kwarai. Na lura cewa lallai idan muna san kasar mu ta ci gaba to wajibi ne mu baiwa harkar ilimi mahimmanci. Ingataccen ilimi shi zai tabbatar da ingantacciyar rayuwa da kuma ingantacciyar makoma. Shi zai kawo kwararru da gogaggun ma’aikata. A takaici ilimi zai taimakawa mutum ya samu ci gaba, sannan al’ummar sa ma ta samu ci gaba.

A karshe bari in koma inda na faro; wato batun mahimmancin bayani. Ban sani ba ko dai aikinmu na ba da labarai da bayani - ba sani ba sabo – ne ya sa Malam Bashir ya yi mani tambaya. Allahu a’alam. Abunda dai na yi imani da shi, shi ne, tambayar sa ta sa ni sake tunani kan mahimmancin ilimi ga al’ummata ta yankin arewacin Nigeria, wadda kuma dukkanin alkaluma ke nuni da cewa ta na baya kwarai da gaske, idan aka kwatanta da yankin kudancin Nigeria.

Facebook | Akwai bukatar amsa...

Facebook | Akwai bukatar amsa...

Sunday 28 February 2010

Kiwon Lafiya a Arewacin Nigeria


A shirin BBC Hausa na safiyar yau an yi wani labari da ya taba ni sosai. Labarin shine na wasu iyaye mata dake dawainiya da 'ya'yan su dake da cutar amosanin jini wato “sickle cell” a turance. Dan jaridar BBC Nura Mohammed Ringim yayi hira da wata mace Hajiya Ba'adiya Magaji wadda dan ta ya rasu shekaru ukun da suka shige, yana mai sheharu talatin da biyar a duniya. Ita kuwa Hajiya Umma Tukur Unguwar Sarki ta na da yara 7 wadanda dukkanin su ke fama da amosanin jini. Ta ce “kafin wata 9 suke nuna alamun ciwon, kuma su na bukatar abincin mai kyau, a kullum su na cikin rigar sanyi saboda ba sa san sanyi, ba sa san wahala”. Wannan uwa ita ce ke kici-kici domin tabbatar da yaran ta suna cikin yanayin da zai hana ciwon ya tashi, abunda ake kira da turanci "crisis” kamar yadda ta shaida.

Watanni biyu da suka shige ni ma wata aminiya ta a Kano ta hadu da rashi sakamakon wannan cuta. Mahmud Kyauta dan aminiyar ta wa ya rasu yana mai shekaru 19 a duniya. Zai shiga jami’a a bana amma sai ciwo ya tashi, aka kai shi asibiti a Kano, cikin ‘yan sa’o’i kadan Allah yayi masa cikawa.

A matsayi na na uwa, na ji wa aminiyar tawa. Domin rashin da mai shekaru 19 a duniya ba karamin abu bane. Na yi ta kokarin ba ta magana da nufin kwantar mata da hankali...dadin abun, a gida, arewacin Nigeria, dangi da makobta kan taimaka a irin wannan lokaci mai wahala. Kodayake dai imani da Allah shine ma babban kushin dake tausasa zuciya.

Sai dai abunda na fahimta shine duk da hanyoyin samar da bayanai na zamani, ga kuma uwa-uba radiyo, har yanzu jama’a a yankin arewacin Nigeria suna da karancin sani ko ilimi kan wannan cuta, wadda ko shakka babu ke ragargazar iyaye da yara.

Amosanin jini in ji masana, cuta ce da ake gada daga iyaye. A takaice matsale ce dake hana zagayawar iska Oxygen a jinin dan Adam. Wannan rashin zagaye na Oxygen a jini kan haifar da ciwo mai tsanani ga mai cuta. Ciwon kan tashi ne musamman idan mutum ya na fama da mura, ko wata ‘yar larurar ko kuma idan ma yayi wani aiki da ya jigata shi.

Masana suna cewa amosanin jini kan kawo lalacewar wasu mahimman injinan dake motsa jikin bil Adama kamar hanta, koda, huhu, zuciya da fatsarmama – abunda kuma suke janyo matsanancin ciwo a kasusuwa jiki. Masu amosanin jini kan yi saurin kamuwa da wasu cututtukan na daban saboda gaukuwar jikin su ba ta da karfi – ma’ana suna da saurin laulayi.

Daga jerin wadannan matsaloli zaka fahimci cewa duk iyayen da Allah ya baiwa yaro ko yara masu fama da amosanin jini, to lallai jidali ya same su.

Anan Birtania akwai babbar kungiya ta masu fama da kuma kula da cutar amosanin jini. Bayanai daga shafin su na intanet ya nuna ba sa kasa a gwiwa wajen gudanar da ayyukan da suka hada da ilmantarwa, wayar da kai, tarukan karawa juna sani, kafa gidauniya dan gudanar da ayyukan bincike kan cutar da dai sauransu. Bayanan kungiyar suka kuma ce babban abunda suka yi imani da shi shine, duk masu cutar amosanin jini na da ‘yancin a basu kulawar da ta kamace su. Suka kuma ce ba sa nuna kyama ko banbanci dan kai “dan kasa ne” ko a’a; ko kuma dan jinsin ka daban da na turawa.

Wannan abun sha’awa ne kwarai, kuma ya sa ni na yi tunani a game da labarin da BBC Hausa suka bayar na kokarin da kungiyoyi irin wadanda aka yi rahoto akan su a yau suke yi a Arewa, wajen samar da yanayi kwatankwacin abunda na karanta a shafin intanet din kungiyar amosanin jinin Birtania.

Amma babban abunda ya sanyaya mun jiki shine sanin cewa harkar kiwon lafiya a Nigeria musammman ma a Arewa din ta na cikin halin da bai dace ba. Muna fama da karancin likitoci, kayayyakin aiki, magunguna da ma dakunan shan magani a yankunan karkara. Haka kuma saboda taluci ya yiwa jama’a katutu, so tari ma iyaye hakura suke yi da kai yara asibiti. Abunda ya ta’azzarar lamarin shine masu fama da cutar amosanin jini na bukatar abinci mai gina jiki saboda kara masu kuzari da rage masu yiwuwar kamuwa da cuttuka. A zahiri dai jama’a na fama da abunda zasu ci sau daya ma a rana. Kididdigar Majalisar Dinkin Duniya ta shekarar 2007 na cewa kashi 70 cikin 100 na ‘yan Nigeria na rayuwa a kasa da dalar Amruka guda a rana wato Naira 140.

Tambayoyi anan sune: yaya jama’ar yankin arewacin Nigeria zasu tunkari matsalar cututtuka ba wai kawai amosanin jini ba, a’a har ma da sauran cuttuka barkatai da jama’a – yara da manya – ke fama da su? Yaya mahukunta zasu samar da ‘yancin jama’ar su na ba su kiwon lafiyar da ya kamace su a matsayin su na ‘yan Adam da kuma ‘yan kasa? Hakkin wanene ya tabbatar da cewa hukumomi sun cika aikin su na kare hakkin jama’a, tare da sauke nauyin dake kansu? Su kuma al’ummar mu wace rawa zasu iya takawa? Ta yaya zasu taimakawa kansu wajen samun hakkin su na ingantaccen kiwon lafiya? Shin mazaje na bayar da tallafi ga matan su, ko kuwa suna sakarwa matan duk nauyi da wahalhalu ta yadda a wasu lokuta matan ke rasa inda zasu saka kan su? A game da cuta amosanin jini, suna sane da cewa idan suka yi gwajin jini kafin su yi aure zasu iya kaucewa samun yaran da zasu kasance masu fama da cutar?

A tunani na wadannan kadan ne daga cikin dinbim tambayoyin da ya kamata mu yi kokarin amsawa wajen tunkarar cutar amosanin jini da sauran cututtuka a Arewacin Nigeria.

Saturday 27 February 2010

Zamani Riga



Allah dai shi yake kawo zamani. Kuma lallai tun da ya ba mu kwakwalwar yin tunani wajibi ne mu yi amfani da ita domin mu ga yadda zamu iya cin gajiyar abubuwan zamani domin samun ci gaba. Idan an ce ci gaba ba wai kawai samun alheri na duniya ba. A’a harma na lahira.

Lallai ci gaba ta fannin fusaha ya kawo abubuwa da yawa. Ya kawo gagaruman ci gaba ga rayuwar dan Adam. Babbar abar da kowa ke magana akan ta a wannan zamani da muke ciki ko kuma karni na ashirin da daya (21st Century) itace duniyar Gizo ko kuma Intanet. Bincike kala-kala ne suka kai ga samun intanet a duniya. Wadanda suka fi yin fice su ne wadanda Donald Davies da Paul Baran da Leonard Kleinrock suka yi. A 1982 ne aka fara jin kanshin abunda ake kira yanar Gizo a kasuwa. Amma sai a shekarun 1990 ne yanar Gizo ta bunkasa. A yau wasu na kiran wannan gagarabadan ci gaba da sunan “juyin-juya-hali”. Ina mai yadda da wannan ikirari domin kuwa a yau kusan babu bayanin da dan Adam zai nema ya rasa a intanet.

Duk da samun nasara a shekarun da yanar Gizon ta kunno kai, masu bincike a kasashen da suka ci gaba ta fannin fusaha sun ki komawa waje guda suce “ai mun ci galaba, bari mu tsaya anan”. A’a sai suka ce bari kuma mu duba yadda wata fusahar zata iya hawa kan wannan nasara da muka samu domin muga kuma inda sabon gwajin zai kaimu”. A sabili da haka ne masu bincike a dakunan bincike na jami’o’i da kamfanoni a kasashe kamar su Amurka, Japan, Sweden, Birtania, Faransa, Germus da sai sauransu, suka shiga gasa da juna wajen kera wayoyin hannun (salula) da zasu iya daukar fusahar intanet. Dama dai tuni irin wadannan wayoyi sun fara siddabaru kamar aikewa da sakonnin tes (text ko sms) da kuma daukar hoto.

A yau wayoyin zamani na aikewa da sakonnin murya da tes, kana suna nadar magana, daukar hotuna da bidiyo. Har wa yau suna da dakunan ajiye bayanan da suka hada da dubban lambobin wayoyin jama’a da sauti. Alal misali zaka iya adana gabadayan Al-Kur’ani mai tsarki akan wayar salula.

Riba ga al’umma ta dangane da wannan ci gaba ba kadan ba ce. Ka iya samun bayanai iri-iri ciki harda kayan koli ko masarufi, firashin kayayyaki, kasuwanni, asibitoci, makarantu da sauransu. Yanzu kuma kafafen yada labarai kamar su BBC, CNN, Al-Jazeera da sauran su, suna kutsawa inda suke neman tabbatar da samar da rahotanni ta hanyoyi daban-daban (wato sauti, tes, hoto da bidiyo).

Dama dai Hausawa mutane ne masu neman ilimi da san sanin abunda duniya ke ciki. Wannan ne ma ya sa suke ma’abuta sauraron radiyo. Abun sha’awa shine sun karbi sabuwar fusahar intanet da wayar salula da hannu bi-biyu, inda suke samun labarai, rahotanni tare da yin musayar ra’ayi da jama’a ba wai kawai a kauyukan su, ko garuruwan su ko kasashen su ba. A’a har ma a duk fadin duniya.

Ni ina ganin idan muka tsaya muka dage wajen amfani da fusahar zamani ta hanyoyi masu kyau, to kuwa babu shakka damu zamu samu gagarumin ci gaba a rayuwar mu kuma mu yi gasa da kowacce al’umma a duniya.

Kada na manta: BBC za ta gabatar da wasu jerin rahotanni na musamman na tsahon makonni biyu kan yadda intanet ta zama gababadau a wannan zamani na mu. Dan samun karin bayani sai kuje wannan shafin: http://bbcsuperpower.com/

Banbancin Mutum da Dabba


Da sunan Allah mai Rahama da Jin Kai. Na fara wannan kundi ne da nufin bayyana tunani na, da fahimta ta a game da abubuwan da na ci karo da su a rayuwa.

Shi dai Mahaliccin mu ya bamu kwakwalwa domin yin tunani kuma so tari ina jin ana fada tun ina karama cewa banbancin mutum da dabba shine tunani. A lokacin da nake girma sai nake nazari akan wannan furuci: "banbancin mutum da dabba shine tunani". Hakika haka maganar take.

Sai dai kuma da girma ya zo mani musamman bayan da na fara rayuwa a kasar yammacin duniya inda dabba take da hakki kusan daidai da na bil Adama, sai na fara kallon dabba daga wani bangare. Tun sannan na gano cewa ashe itama dabba tana da tunani kamar mutum. Alal misali ta san mai ba ta abinci, ta san mai korar ta. A sannan ne kuma na fara tunanin cewa mai yiwuwa banbancin mutum da dabba shine: mutum yana iya wasu abubuwa wadanda dabbobi basa yi kamar ikon magana da rubutu da karatu.

Wannan shine arzikin da dan Adam yake da shi: ikon tunani, mu'amala da sauran jama'a, karatu da rubutu, sannan ya hada wadannan hikimomi domin ciyar da rayuwar sa gaba.

Ci gaba shine ginshikin rayuwar mutum. Babu wanda yake san halin "jiya-i-yau". Ko rashin lafiya mutum ke fama da shi yana neman samun sauki, idan Taro kake da shi kana neman ya zama Sisi, idan tumakin ka biyu kana so su zama shidda, idan makota kake shiga debo ruwa to kana san Allah ya hore maka ta yadda zaka haka taka rijiyar a cikin gidan ka, idan a unguwar ku tsibirin shara ya dame ku kana so hukuma ta kirkiro da wani shiri da zai tabbatar da tsaftace muhallin ku...Tambayar anan itace shin kai da ni da kowa na amfani da irin hikimomin da Allah ya hore mana a matsayin mu na bil Adama wajen kawo ci gaba, ba ga rayuwar mu kawai ba, a'a, har ma ta al'ummar mu gabakidaya? A zahiri akwai ayar tambaya.

Mai yiwuwa tunanin ku ya banbanta da nawa...amma ni a ta wa 'yar fahimtar wannan shine tunani dan kalilan na Almajira.

Almajira


Wannan kundi zai dora duk wani abu da ya shafi ci gaban dan Adam daga fahimtar Almajira daga yankin Arewacin Nigeria.