Matattarar ra'ayi, da tunani kan al'ummaran yankin Arewa, da Nigeria da sauran sassan duniya.
Showing posts with label Azumi Talauci Nigeria. Show all posts
Showing posts with label Azumi Talauci Nigeria. Show all posts
Friday, 15 July 2011
Ga Tashin Bama-Bamai ga Watan Ramadan
Halin da ake ciki yanzu haka a wasu yankun nan Arewacin Nigeria musamman ma Maiduguri ya kai abunda zamu ce “Inna Lillahi wa inna ilaihir rajiun”. Tashe tashen hankula sakamakon tashin bama-bamai da kuma samamen da ake kaiwa kan wadanda ake zaton yan kungiyar Boko Haram ne sun sanya matsanancin tsoro da fargaba a zukatan jama’a.
Ana ta muhawara kan yaya aka yi har aka kai wannan mummunan hali da ake ciki. Ni a ganina wannan ihu ne bayan hari. A madadin tambayar yaya aka yi aka kai haka. Kamata yayi a maida hankali kan yadda za’a samo maslaha domin kawo karshen wannan hali da ake ciki.
Sai dai kuma ko wannan ma ba karamar tambaya ba ce. Shin yaya ake ganin za’a iya magance matsalar? Ta ina za’a faro? Shin tattaunawa ya kamata ayi? Idan tattaunawa ce tsakanin wa da wa za’a yi? Kuma idan za’a yi tattaunawar su wanene zasu wakilci gwamnati, su wanene zasu wakilci ‘yan kungiyar ta Boko Haram?
A jiya an rawaito kungiyar tuntubar juna ta Arewa wato Arewa Consultative Forum ta na cewa zata baiwa shugaban Nigeria Goodluck Jonathan shawara kan yadda ta ke ganin ya kamata a tunkari matsalar ta Boko Haram.
Sai dai a wani lamari tamkar arashi, a yau sai kungiyar matasan Arewa wato Arewa Youth Forum suka fitar da wata sanarwa suna masu kakkausar sukan dattawan na Arewa. Suka ce ai dattawan basu da hurumi, halarci ko iyawa a game da yadda za’a warware matsalolin Arewa. Kungiyar ta ce ai tun da farko su dattawan Arewan ne suka jefa yankin cikin mummunan halin fatara da jahilcin da ake ciki. Amma yanzu kiri da muzu, sun zo su na maganar magance matsalar.
To lallai dai masifar da ake ciki a yankin Arewa ta Nigeria ba jiya ko shekaranjiya ta samo asali ba. Matsala ce da ta jima tana ci, can daga karkashi. A shirin BBC Hausa a Karkara na Maris 2009, na jagorancin ‘yan jaridar BBC Hausa inda muka ganewa idanuwan abubuwan da suka saka mu hawaye. A shirin BBC Hausa a Karkara na karshe na bayyana cewa Arewacin Nigeria na zaune akan bam wanda a kowanne lokaci zai iya tashi.
A wanncen lokaci wasu sun ce muna yiwa kasa mugun alkaba’i. Abun takaicin shine, sun kawar da idanun su daga halin talauci, rashin aikin yi, shaye-shayen miyagun kwayoyi, da watangaririyar da ‘ya’yan bayin Allah ke yi a yankin. A karshe ga halin da muke ciki a yau.
To babban jawabi na a wannan sharhi, shine, kamar kowa, ina yin roko na cewa yayinda watan ibada mai tsarki na watan Ramadan yake karatowa, shugabanni da ‘yan kungiyar Boko Haram, su dubi girma Allah Subhanu wata’ala, su nemi hanyar kawo zaman lafiya, hanyar da za’a wanzar da adalci tsakanin al’umma. Wannan shine kadai zai kawo zaman lafiya mai dorewa.
Monday, 16 May 2011
Zaben 2011: Wancakalar da Babbar Dama
Zaben Nigeria na 2011 ya zo, ya tafi, ya kuma bar baya da kura. Babban makasudin wannan kura kuwa itace burin da jama’a suka dauka suka dorawa shugaban hukumar zaben da aka nada da zummar gudanar da zabuka masu inganci a kasar wato Farfesa Attahiru Jega, da kuma cewa a bana zasu yi amfani da kuri'arsu a matsayin babbar dama ta zabar wadanda zasu fish-she su daga halin la-haulan da suke ciki.
Kafin nada Jega 'yan Nigeria, da ma duniya gabakidaya, sun yi ittifakin cewa zabukan da aka yi a kasar a shekarun 2003 da 2007 ba wani abu bane, illa bankaura. Masu sa idanu kan wadancen zabukan sun bayyana cewa sune mafi muni a tarihin jefa kuri’a a Nigeria. Masu fafutukar wanzar da democradiyya a ciki da waje sun ta kokawar ganin an sauya tsarin zabe a Nigeria ta yadda zasu kasance ingantattu. Shi kansa shugaban da aka ce shi ya lashe zaben na 2007, marigayi Umaru Musa Yar’adua ya amince kan cewa lallai akwai bukatar yin gyara.
Saboda haka, bayan kasashen duniya musamman Amurka sun hurawa Nigeria wuta sai shugaba Goodluck Jonathan ya kawo Attahiru Jega a matsayin wanda zai gudanar da ingantattun zabuka a kasar. Sakamakon sunan da yayi a jami’a a matsayin “dan akida” da “taurin kai” sai jama’a suka ce, to zabe mai nagarta zai yiwu a Nigeria.
Sai dai tun sannan masu sharhi kan al’amuran siyasa a Nigeria kamar Dakta Junaidu Mohammed suka bayyana shakkunsu dangane da hakan. Suna masu cewa ai gyara ba zai yiwu idan mutun daya ne tak yake da manufar yin sa ba. Masu irin wannan ra’ayi sun dage kan cewa muddin dai ana san gyara, to wajibi ne Jega ya kori ma’aikatan hukumar zaben kasar INEC wadanda suka yi aiki a karkashin tsohon shugaban hukumar wanda ake yiwa kallon mazambaci wato Farfesa Maurice Iwu. Hakan dai bai faru ba.
A karshe dai ‘yan Nigeria sun kama hanyar jefa kuri’a ranar asabar 2 ga Afrilu, amma sai me? Ana tofa bisimillah, sai kwatsam, aka ba da sanarwar an dage zaben zuwa mako na gaba. Tun daga sannan ne gwiwowin jama’a da dama suka yi sanyi. A dan wannan lokaci an yi zargin kama manyan motoci makare da takardun zabe, da cewa sun yi sama ko kasa. Haka kuma jam’ian tsaro suma sun ta yin kalamai da suka ci karo da juna wadanda tun daga sannan jama’a suka ce, an ya kuwa?
Allah cikin ikonsa an yi zaben a haka – cikin zarge-zarge da fargaba, da tashe-tashen hankali, da abubuwan da ba zasu fadu ba.
Sai dai babban abunda ya fito wanda kuma shine babban abun takaici a wannan zaben shine yadda aka yi amfani da kudi, da kayan masarufi kamar sabulun wanka da shinkafa da taliyar Indomie, kiri-kiri a bainar jama’a, ba kunya, ba tsoro, dan jan hankalin masu zabe su zabi jam’iyyar da ke rabon kudin da kayan masarufin.
Abun bakin ciki shine, talauci da mutuwar zuciya sun yi tasiri, inda jama’a suka sa kafa suka shure damar da suke da ita ta kawo sauyi. A karshe sun zabi wadanda suka basu kudin da zai biya masu bukatar ‘yan kwanaki kilalan, a madadin wadanda ake ganin zasu kawo gyara na zahiri a kasa.
Wannan gajeren tunani ne a bangaren talakawa. Ba su tuna cewa wadanda suka basu kudin nan ba sune wadanda suka sa kafa suka dannan su cikin kuncin da suke ciki. Ba su tuna cewa kudin nan da aka dauko aka sammu su, dama nasu ne ba, wanda kuma da sune ya kamata a samar musu da wuta da ruwa da asibi da makarantu, amma aka ki yin hakan, sai da zabe yazo aka dan guzutso aka basu domin su mayar da yawu.
To a karshe talakawan Nigeria, da taimakon wadanda suka jefa su cikin kangin wahalar da suke ciki, sun wancakalar da damar da suka samu a 2011. Abunda yayi saura shine ko wadanda suka zaba a bana zasu fitar dasu daga matsanancin halin rayuwar da suke ciki ko a’a?
Da yace an ce Allah ya na baiwa al’umma shugabanni irin jama’arta, fatan mu kawai yanzu shine Ubangiji, Allah ya cece mu, Ya kawo mana sauyi tun daga cikin zukatanmu, mu kanmu, wanda kuma a karshe shi zai kaimu ga samun adalan shugabanni da zasu ciyar da kasar mu gaba.
Tuesday, 5 April 2011
Kancal A Shirin Zaben Nigeria
Zaben Nigeria na ci gaba da jan hankali a ciki da wajen kasar saboda dalilai da yawa. Kuma yanzu, fiye da kowanne lokaci, na yi imanin cewa duk kokarin mutum na kawo gyara a kasarmu, sai wasu sun yi kokarin kawo cikas, ko yin kancal!
Kowa dai ya san Profesa Attahiru Jega shugaban hukumar zaben Nigeria wato INEC, mutum ne mai akida. Kuma idan ya dage kan abu, ba’a iya tankwara shi.
Allah dai ya kai shi INEC, kuma tun sannan wasu suke cewa mai yiwuwa saboda akidarsa a samu ingantattun zabuka a Nigeria. Sai dai kuma wasu na cewa shi kadai ba zai iya kawo gyara ba. Inda masu musun farko ke cewa ai shugabanci na iya sauya na kasa. Ni ma ina daga cikin wadanda suka yi wannan fata.
Sai dai yayinda ni da sauran abokan aikina a BBC muka shirya kawowa ‘yan Nigeria rahotannin zaben da aka shirya yi a 2 ga watan Afrilu, sai kwatsam rahotannin matsaloli. A karshe dai an dage zabukan.
Dage zabukan sakamakon cikas din da aka samu abu ne da ya girgiza mutane da yawa. Sai dai mafi yawan ‘yan Nigeria na ci gaba da baiwa Jega goyon baya, suna masu cewa muddin dai zabukan zasu kasance na fisabilillahi, to ai dage su ba wani ba ne.
Ana dai ta hasashe da zarge-zarge cewa akwai wasu da suka hadiyi layer cewa zabukan nan ba zasu yi nasara ba ko ta halin hakaka saboda dalilan san-kai ba na san kasa ba. Idan haka ne Allah ya yi maganinsu domin bayin Allah.
A karshe ya zaman wajibi jam’ar Nigeria su jajirce wajen tabbatar adalci da samun shugabanni na gari.
Monday, 23 August 2010
Wasu na Shan Ruwan Bunu a Watan Azumi, Wasu na Shan Kindirmon Kwali

Watan Azumi wata ne mai alfarma ga dukkanin Musulmi a koina a cikin duniya. Kuma yau, a kwana a tashi, gashi har wata yana neman rabawa. A duk tsahon wannan watan BBC Hausa tana kawo rahotanni da sakonnin “shan ruwa daga masu sauraron mu”.
Wasu sun aiko mana da tambaya suna cewa mecece fa’ida ko hikimar kawo sakonnin “shan ruwa daga masu sauraron mu?” To lallai ga wanda bai kalli lamarin cikin zurfin tunani ba zai ga tamkar ba wani abu ba ne illa kawai kawo mutane suna cewa sun ci kaza sun sha kaza. A saboda haka kenan wannan ba abu ne mai mahimmanci ba.
Sai dai ni kuwa ba haka nake kallon abun ba. Ina kallon sa ne daga fannin launin abincin da mafi yawan jama’ar mu ke ci a wannan wata mai tsarki bayan sun kamalla ibadar su da magariba.
Kowa dai ya wuni da azumi, zai so ya yi buda baki da dan abun marmari da kuma ababen gina jiki wadanda zasu mayar da gurbin abunda aka rasa a yayin azumin. Sai dai sauraron irin abunda da mafi yawan al’ummar Hausawa ke shan ruwa da su, abu ne dake kawo hawaye a ido.
“Ni dai yau na sha ruwa da ruwan bunu da rama; yau na ci dabino da kunun kanwa, illa iyaka; ni dai na sha ruwa da dan-wake da mai da yaji, iyakar abunda Allah ya hore min kenan, Allah ya nuna mana gobe lafiya!”
Wadannan sune kadan daga dubban sakonnin da BBC Hausa ke samu a kowanne dare. Me sakonnin suke nuna mana? Lallai suna yin nuni ne da irin wahalar da jama’a suke ciki a kasar mu. Kuma yayinda miliyoyi ke shan “ruwan bunu” wasu ‘yan tsiraru kuwa suna shan kindirmon kwali mai sanyi da naman kaji.
Nigeria dai ba kasa ce matalauciya ba. Amma kuma jam’a na cikin halin matanancin talauci. An san dalilan da suke janyo talaucin: rashin shugabanci na-gari, rashawa, almundahana, rashin adalci da tsananin san-kai. Kididdgar Majalisar Dinkin Duniya na cewa mafi yawan ‘yan Nigeria na rayuwa ne akan kasa da Dala daya – wato kasa da Naira 150 - a rana.
A wannan lokaci na ibada kamata yayi mu kara tunani a game da halayyar mu ko Allah zai ji tausayin mu. Mu gyara halayen mu sannan kuma mu roke Shi Ya ba mu shugabanni masu tausayin talakawa, wadanda zasu fitar da al’ummar mu daga kangin talauci.
A sha ruwa lafiya!
Subscribe to:
Comments (Atom)


