Showing posts with label Shara Kano Birane Nigeria. Show all posts
Showing posts with label Shara Kano Birane Nigeria. Show all posts

Saturday, 27 March 2010

Tilin Shara a Biranen Mu


Ban sani ba ko wani zai gane wannan tilin sharar dake wannan hotan. To wannan dai wata unguwa ce a birnin da yafi kowanne girma a nahiyar Afrika. Wato birnin da na fito, birnin da aka haife, Kano.

Kusan ta kowanne bangare Kano shine birnin da ya fi kowanne birni a Nigeria. Wannan ma shi ya sa ake masa kirari da: Kano, ko da mai ka zo an fika. Sai dai kuma tsakani da Allah, ba komai ne ya kamata a ce birni na, yafi saura akai ba.

Ba alfahari ba ne a ce birni na shi ya fi kowanne kazanta ko tarin shara a Nigeria ko Afrika. Idan na zo da baki ina yawo da su a garin nakan ji matukar kunya. A gaskiya ma, akwai unguwannin da bana bi da su.

Na yadda kan cewa yawan jama’a na taimakawa wajen taruwar shara a kankanin lokaci. To amma musun da nake san yi anan shine, ai idan aka samar da wata hanya kyak-kyawa, mai tsari, ta kwasar shara akan kari, ba tare da bata lokaci ba, to kuwa za’a rage afkuwar matsalar tarin shara a Kano.

A lokacin da nake korafin tilin shara a garin mu, sai na tuna cewa a gaskiya matsalar tarin shara a tsakiyar al’umma ba matsala ce da ta tsaya a Kano kawai ba. A’a!

Kusan ilahirin biranen arewacin Niigeriar da na je a shekarun nan na fama da matsalar shara. Sai dai a ce wasu sun fi wasu.

Tilin shara a tsakiyar al’umma na kawo barazana kala’kala ga bil adama. Alal misali saboda dankarewar sharar da ta hada da tsummokara, leda, bawawwaki, dusa, kashin awaki, takardu, kai da duk wani abu maras amfani, wadanda akan jigba akan magudanan ruwa, sauro ke cin karen sa ba babbaka. Sakamakon wannan kuwa itace cutar cizon sauro wato Malaria a turance.

Abun da kan bani mamaki kuma shine yadda zaka ga masu suyar kifi ko balangu sun soye-soye ko gashe-gashen su a dab da tilin sharar. Kuma mutane suna ta siya ba tare da tunani hakan na iya janyo musu cuttukar kamar su amai da zawo da Thypoid ba.

Haka kuma sai ka ga yara da matasa suna tsince-tsincen robobi ko rafta – kamar yadda ake cewa a Kanon – dan siyarwa.

Idan hukuma na da laifi, suma jama’ar unguwa da gari suna da nasu laifin. Menene ya sa ba za’a hada kai, a fitar da wani tsari da zai tabbatar da jama’a ba sa zubar da shara a ko ina ba sai inda hukuma ta shata? Me yasa mutane basu damu da kiwon lafiya da tsaftar muhallin su ba?

Mai yiwuwa wasu su ce ai matsalar shara kadan ce, akwai wadanda suka fi ta girma. Amma a nawa tunanin wannan ma matsala ce musamman tun da tana barazana ga lafiyar al’umma.

Me ya kamata mu yi akan matsalar shara a biranen mu? Zan so in ji daga duk mai shawara.