Showing posts with label Boko Haram. Show all posts
Showing posts with label Boko Haram. Show all posts

Friday, 15 July 2011

Ga Tashin Bama-Bamai ga Watan Ramadan



Halin da ake ciki yanzu haka a wasu yankun nan Arewacin Nigeria musamman ma Maiduguri ya kai abunda zamu ce “Inna Lillahi wa inna ilaihir rajiun”. Tashe tashen hankula sakamakon tashin bama-bamai da kuma samamen da ake kaiwa kan wadanda ake zaton yan kungiyar Boko Haram ne sun sanya matsanancin tsoro da fargaba a zukatan jama’a.

Ana ta muhawara kan yaya aka yi har aka kai wannan mummunan hali da ake ciki. Ni a ganina wannan ihu ne bayan hari. A madadin tambayar yaya aka yi aka kai haka. Kamata yayi a maida hankali kan yadda za’a samo maslaha domin kawo karshen wannan hali da ake ciki.

Sai dai kuma ko wannan ma ba karamar tambaya ba ce. Shin yaya ake ganin za’a iya magance matsalar? Ta ina za’a faro? Shin tattaunawa ya kamata ayi? Idan tattaunawa ce tsakanin wa da wa za’a yi? Kuma idan za’a yi tattaunawar su wanene zasu wakilci gwamnati, su wanene zasu wakilci ‘yan kungiyar ta Boko Haram?

A jiya an rawaito kungiyar tuntubar juna ta Arewa wato Arewa Consultative Forum ta na cewa zata baiwa shugaban Nigeria Goodluck Jonathan shawara kan yadda ta ke ganin ya kamata a tunkari matsalar ta Boko Haram.

Sai dai a wani lamari tamkar arashi, a yau sai kungiyar matasan Arewa wato Arewa Youth Forum suka fitar da wata sanarwa suna masu kakkausar sukan dattawan na Arewa. Suka ce ai dattawan basu da hurumi, halarci ko iyawa a game da yadda za’a warware matsalolin Arewa. Kungiyar ta ce ai tun da farko su dattawan Arewan ne suka jefa yankin cikin mummunan halin fatara da jahilcin da ake ciki. Amma yanzu kiri da muzu, sun zo su na maganar magance matsalar.

To lallai dai masifar da ake ciki a yankin Arewa ta Nigeria ba jiya ko shekaranjiya ta samo asali ba. Matsala ce da ta jima tana ci, can daga karkashi. A shirin BBC Hausa a Karkara na Maris 2009, na jagorancin ‘yan jaridar BBC Hausa inda muka ganewa idanuwan abubuwan da suka saka mu hawaye. A shirin BBC Hausa a Karkara na karshe na bayyana cewa Arewacin Nigeria na zaune akan bam wanda a kowanne lokaci zai iya tashi.

A wanncen lokaci wasu sun ce muna yiwa kasa mugun alkaba’i. Abun takaicin shine, sun kawar da idanun su daga halin talauci, rashin aikin yi, shaye-shayen miyagun kwayoyi, da watangaririyar da ‘ya’yan bayin Allah ke yi a yankin. A karshe ga halin da muke ciki a yau.

To babban jawabi na a wannan sharhi, shine, kamar kowa, ina yin roko na cewa yayinda watan ibada mai tsarki na watan Ramadan yake karatowa, shugabanni da ‘yan kungiyar Boko Haram, su dubi girma Allah Subhanu wata’ala, su nemi hanyar kawo zaman lafiya, hanyar da za’a wanzar da adalci tsakanin al’umma. Wannan shine kadai zai kawo zaman lafiya mai dorewa.

Friday, 17 June 2011

Yaya Za'a Warware Matsalar Boko Haram

Matsalar Boko Haram, matsala ce da kowa yake jin tsoron yin sharhi akai. Dalili kuwa shine suna ganin muddin suka yi magana watakila ‘yan Boko Haram din su kai masu hari. Amma kuma a matsayinmu na ‘yan jarida dole ne mu yi tsokaci dangane da abubuwan da ke faruwa a kasarmu da nufin neman hanyoyin warware wadanda muke ganin matsaloli ne.

Boko Haram ta somo asali yau kusan shekaru 2, inda ake daukar jihar Borno dake arewa maso gabashin Nigeriar a matsayin hedikwatar su. Ana ganin aikace-aikacen ‘yan kungiyar da cewa kokari ne na ganin an kaddamar da Shari’ar Musulunci a Nigeria.

Hare-haren da Boko Haram ke kaiwa sun tsananta ne bayan kashe shugabansu
Mohammed Yusuf da jami’an tsaron Nigeria suka a Yulin 2009. Tun a wancen lokacin ne ‘yan Boko Haram suka sha alwashin daukar fansa tare da yaki da duk wadanda suke ganin makiyin su ne.

Yanzu haka dai abu yayi abu. Boko Haram na kai hari ta ko ina, duk dai a kokarin cimma manufofinsu. A lokacin da ya kai ziyara Amurka, Shugaban Nigeria Goodluck Jonathan ya bayyana a makon da ya gabata cewa yana neman a tattauna da ‘yan Boko Haram din, da nufin kawo karshen tashe-tashen hankulan da ake samu a wasu sassan kasar. Sai dai bayan kalamin na sa, sai aka ambato shugaban rundunar ‘yan sandan Nigeria Hafiz Ringim yana yin barazana ga ‘yan Boko Haram yana mai cewa karyar su ta kusan karewa.

Ana dai bayyana cewa wai wannan furuci ne ya tunzura ‘yan Boko Haram suka kai hari a hedikwatar ‘yan sandan Nigeria dake Abuja. Daga bisani kungiyar ta fitar da sanarwa tana mai daukar alhakin harin bam din da yayi sanadiyyar hasarar rayuwa da dukiya.

To yanzu da aka zo wannan matsaya, ta yaya za’a tunnkari matsalar Boko Haram?

Ni dai har yanzu banga wani wanda a yanzu ya lashi takobin cewa yana da wata cikakkiyar masaniya ba. Amma a matsayin mu na masu sharhi kan al’amuran da suka shafi kasar mu wajibi ne mu nemi ansa ga wasu mahimamman tambayoyi. Wadannan kuwa sune:

Menene ya janyo matsalar Boko Haram? Su wanene ‘yan Boko Haram? Ta yaya za’a fara tattaunawa da su domin neman sulhu? Yaya shugabannin Nigeria zasu kasance masu tausayin jama’ar su ta yadda jama’a zasu daina yi musu kallon makiya? Yaya ‘Yan Nigeria suke san makomar kasarsu a gajeren lokaci da kuma a shekarun gaba ya kasance? Wadanna matakai za’a dauka na zahiri ba abunda Fulani suke cewa “foululu” kawai ba?

Bayan mun yi wadannan sai mu hada da addu’ar neman Allah ya kawo mana zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar mu Nigeria.