Matsalar Boko Haram, matsala ce da kowa yake jin tsoron yin sharhi akai. Dalili kuwa shine suna ganin muddin suka yi magana watakila ‘yan Boko Haram din su kai masu hari. Amma kuma a matsayinmu na ‘yan jarida dole ne mu yi tsokaci dangane da abubuwan da ke faruwa a kasarmu da nufin neman hanyoyin warware wadanda muke ganin matsaloli ne.
Boko Haram ta somo asali yau kusan shekaru 2, inda ake daukar jihar Borno dake arewa maso gabashin Nigeriar a matsayin hedikwatar su. Ana ganin aikace-aikacen ‘yan kungiyar da cewa kokari ne na ganin an kaddamar da Shari’ar Musulunci a Nigeria.
Hare-haren da Boko Haram ke kaiwa sun tsananta ne bayan kashe shugabansu
Mohammed Yusuf da jami’an tsaron Nigeria suka a Yulin 2009. Tun a wancen lokacin ne ‘yan Boko Haram suka sha alwashin daukar fansa tare da yaki da duk wadanda suke ganin makiyin su ne.
Yanzu haka dai abu yayi abu. Boko Haram na kai hari ta ko ina, duk dai a kokarin cimma manufofinsu. A lokacin da ya kai ziyara Amurka, Shugaban Nigeria Goodluck Jonathan ya bayyana a makon da ya gabata cewa yana neman a tattauna da ‘yan Boko Haram din, da nufin kawo karshen tashe-tashen hankulan da ake samu a wasu sassan kasar. Sai dai bayan kalamin na sa, sai aka ambato shugaban rundunar ‘yan sandan Nigeria Hafiz Ringim yana yin barazana ga ‘yan Boko Haram yana mai cewa karyar su ta kusan karewa.
Ana dai bayyana cewa wai wannan furuci ne ya tunzura ‘yan Boko Haram suka kai hari a hedikwatar ‘yan sandan Nigeria dake Abuja. Daga bisani kungiyar ta fitar da sanarwa tana mai daukar alhakin harin bam din da yayi sanadiyyar hasarar rayuwa da dukiya.
To yanzu da aka zo wannan matsaya, ta yaya za’a tunnkari matsalar Boko Haram?
Ni dai har yanzu banga wani wanda a yanzu ya lashi takobin cewa yana da wata cikakkiyar masaniya ba. Amma a matsayin mu na masu sharhi kan al’amuran da suka shafi kasar mu wajibi ne mu nemi ansa ga wasu mahimamman tambayoyi. Wadannan kuwa sune:
Menene ya janyo matsalar Boko Haram? Su wanene ‘yan Boko Haram? Ta yaya za’a fara tattaunawa da su domin neman sulhu? Yaya shugabannin Nigeria zasu kasance masu tausayin jama’ar su ta yadda jama’a zasu daina yi musu kallon makiya? Yaya ‘Yan Nigeria suke san makomar kasarsu a gajeren lokaci da kuma a shekarun gaba ya kasance? Wadanna matakai za’a dauka na zahiri ba abunda Fulani suke cewa “foululu” kawai ba?
Bayan mun yi wadannan sai mu hada da addu’ar neman Allah ya kawo mana zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar mu Nigeria.
Matattarar ra'ayi, da tunani kan al'ummaran yankin Arewa, da Nigeria da sauran sassan duniya.
Showing posts with label Hausa. Show all posts
Showing posts with label Hausa. Show all posts
Friday, 17 June 2011
Wednesday, 15 June 2011
EFCC KO KYANWAR LAMI
Yau shugabar hukumar yaki da laifukan da suka danganci ta’annati da dukiyar jama’a a Nigeria wato EFCC ta yi bikin cika shekara 8 da kafuwa. Shugabar ta zayyana irin kokarin da hukumar ta su ta yi, wajen zakulo wadanda ta kira miyagun da suke wawaso da dukiyar jama’a.
Hukumar ta kara da lasafta sunayen manyan mutane, musamman ma tsoffin ministoci da gwamnoni da wasu ‘yan kasashen waje da suke da uwa a gindin murhu- wato manyan jami’an gwamnatin Nigeria - a matsayin shaidar kokarin da suke yi na sa kafar wando guda da duk wannda ya yiwa dukiyar Nigeria karan tsaye.
Lallai wannan ba karamin abu bane a kasar da cin hanci ya zame mata jini da tsoka. Ko a cikin ‘yan kwanakin nan sai da jami’an tsaro suka yi artabu da tsohon kakakin majalisar wakilan kasar Dimeji Bankole kafin su kama shi a makon jiya. Hukumar EFCC din na zargin Bankole da barnatar da kudin da suka haura Naira biliyan 40.
A gaskiya dai duk da kokarin da EFCC ta ce tana yi, jama’ar Nigeria na ci gaba da yi mata kallon wata wadda ke da manufa ta karkashin kasa. Allal misali a yanzu haka da akwai wadanda suke zargin cewa wai ana tuhumar Bankole ne saboda ya ja ragamar ‘yan majalisar da suka sauya dokar zaben kakakin majalisa. Shi kuma wannan sauyi da majalisar ta yi, shi ya kai ga wancakalar da shirin karbi-in-karba, lamarin da ya batawa jam'iyyar PDP rai.
To, ko ma dai wane kallo ake yiwa EFCC, mutane masu yawa na ganin, kamata yayi hukumar ta daina kwakwazo, ta kama mutum, kana sai a ji shiru. A madadin haka idan aka kama mutum, sai a kaishi kotu, a yanke masa hukunci, sannan a bayyanawa jama’a hukuncin da aka yanke masa, saboda ya zama darasi ga saura. Har yanzu kalilan ne a cikin manyan mutanen da EFCC ta bayyana sunayen su aka gurfanar da su gaban kuliya kana aka yanke musu hukunci. So tari maganar shiriricewa take yi kawai.
A karshe muddin dai EFCC na san ta yaki ta’annati da dukiyar jama’ar Nigeria, to wajibi ne ta tabbatar ta ga karshen zargin wawason da ake yiwa mutane, sannan ta bayyanawa duniya hukuncin daurin da aka yiwa mutum. Baya ga wannan sai kuma sauran hukumomi su buga sitamfi akan mutumin nan da aka yankewa hukuncin, da cewa: muddin aka kama ka da laifi, kana aka hukunta ka bisa laifin satar dukiyar bayin Allah, to kuwa kayi sallama da rike mukami a Nigeria, komai kankantarsa.
Muddin ba’a yi haka ba, kowa zai ci gaba da kwasar ganima saboda ya san cewa bayan an kamala hayaniya a kafofin yada labarai, zai kwana kalau. Watakila bayan ‘yan watanni ya tsaya takarar mukami, kuma a ganshi mirsisi wai yana rike da matsayin mai yin doka a kasa, ko ya zama shugaban al’ummar da ya taba cuta a matakin jiha ko kasa.
A yayinda ta cika shekara 8 da kafuwa, dole EFCC ta guji kasancewa Kyanwar Lami.
Monday, 16 May 2011
Zaben 2011: Wancakalar da Babbar Dama
Zaben Nigeria na 2011 ya zo, ya tafi, ya kuma bar baya da kura. Babban makasudin wannan kura kuwa itace burin da jama’a suka dauka suka dorawa shugaban hukumar zaben da aka nada da zummar gudanar da zabuka masu inganci a kasar wato Farfesa Attahiru Jega, da kuma cewa a bana zasu yi amfani da kuri'arsu a matsayin babbar dama ta zabar wadanda zasu fish-she su daga halin la-haulan da suke ciki.
Kafin nada Jega 'yan Nigeria, da ma duniya gabakidaya, sun yi ittifakin cewa zabukan da aka yi a kasar a shekarun 2003 da 2007 ba wani abu bane, illa bankaura. Masu sa idanu kan wadancen zabukan sun bayyana cewa sune mafi muni a tarihin jefa kuri’a a Nigeria. Masu fafutukar wanzar da democradiyya a ciki da waje sun ta kokawar ganin an sauya tsarin zabe a Nigeria ta yadda zasu kasance ingantattu. Shi kansa shugaban da aka ce shi ya lashe zaben na 2007, marigayi Umaru Musa Yar’adua ya amince kan cewa lallai akwai bukatar yin gyara.
Saboda haka, bayan kasashen duniya musamman Amurka sun hurawa Nigeria wuta sai shugaba Goodluck Jonathan ya kawo Attahiru Jega a matsayin wanda zai gudanar da ingantattun zabuka a kasar. Sakamakon sunan da yayi a jami’a a matsayin “dan akida” da “taurin kai” sai jama’a suka ce, to zabe mai nagarta zai yiwu a Nigeria.
Sai dai tun sannan masu sharhi kan al’amuran siyasa a Nigeria kamar Dakta Junaidu Mohammed suka bayyana shakkunsu dangane da hakan. Suna masu cewa ai gyara ba zai yiwu idan mutun daya ne tak yake da manufar yin sa ba. Masu irin wannan ra’ayi sun dage kan cewa muddin dai ana san gyara, to wajibi ne Jega ya kori ma’aikatan hukumar zaben kasar INEC wadanda suka yi aiki a karkashin tsohon shugaban hukumar wanda ake yiwa kallon mazambaci wato Farfesa Maurice Iwu. Hakan dai bai faru ba.
A karshe dai ‘yan Nigeria sun kama hanyar jefa kuri’a ranar asabar 2 ga Afrilu, amma sai me? Ana tofa bisimillah, sai kwatsam, aka ba da sanarwar an dage zaben zuwa mako na gaba. Tun daga sannan ne gwiwowin jama’a da dama suka yi sanyi. A dan wannan lokaci an yi zargin kama manyan motoci makare da takardun zabe, da cewa sun yi sama ko kasa. Haka kuma jam’ian tsaro suma sun ta yin kalamai da suka ci karo da juna wadanda tun daga sannan jama’a suka ce, an ya kuwa?
Allah cikin ikonsa an yi zaben a haka – cikin zarge-zarge da fargaba, da tashe-tashen hankali, da abubuwan da ba zasu fadu ba.
Sai dai babban abunda ya fito wanda kuma shine babban abun takaici a wannan zaben shine yadda aka yi amfani da kudi, da kayan masarufi kamar sabulun wanka da shinkafa da taliyar Indomie, kiri-kiri a bainar jama’a, ba kunya, ba tsoro, dan jan hankalin masu zabe su zabi jam’iyyar da ke rabon kudin da kayan masarufin.
Abun bakin ciki shine, talauci da mutuwar zuciya sun yi tasiri, inda jama’a suka sa kafa suka shure damar da suke da ita ta kawo sauyi. A karshe sun zabi wadanda suka basu kudin da zai biya masu bukatar ‘yan kwanaki kilalan, a madadin wadanda ake ganin zasu kawo gyara na zahiri a kasa.
Wannan gajeren tunani ne a bangaren talakawa. Ba su tuna cewa wadanda suka basu kudin nan ba sune wadanda suka sa kafa suka dannan su cikin kuncin da suke ciki. Ba su tuna cewa kudin nan da aka dauko aka sammu su, dama nasu ne ba, wanda kuma da sune ya kamata a samar musu da wuta da ruwa da asibi da makarantu, amma aka ki yin hakan, sai da zabe yazo aka dan guzutso aka basu domin su mayar da yawu.
To a karshe talakawan Nigeria, da taimakon wadanda suka jefa su cikin kangin wahalar da suke ciki, sun wancakalar da damar da suka samu a 2011. Abunda yayi saura shine ko wadanda suka zaba a bana zasu fitar dasu daga matsanancin halin rayuwar da suke ciki ko a’a?
Da yace an ce Allah ya na baiwa al’umma shugabanni irin jama’arta, fatan mu kawai yanzu shine Ubangiji, Allah ya cece mu, Ya kawo mana sauyi tun daga cikin zukatanmu, mu kanmu, wanda kuma a karshe shi zai kaimu ga samun adalan shugabanni da zasu ciyar da kasar mu gaba.
Subscribe to:
Comments (Atom)


