Monday, 23 August 2010

Wasu na Shan Ruwan Bunu a Watan Azumi, Wasu na Shan Kindirmon Kwali


Watan Azumi wata ne mai alfarma ga dukkanin Musulmi a koina a cikin duniya. Kuma yau, a kwana a tashi, gashi har wata yana neman rabawa. A duk tsahon wannan watan BBC Hausa tana kawo rahotanni da sakonnin “shan ruwa daga masu sauraron mu”.

Wasu sun aiko mana da tambaya suna cewa mecece fa’ida ko hikimar kawo sakonnin “shan ruwa daga masu sauraron mu?” To lallai ga wanda bai kalli lamarin cikin zurfin tunani ba zai ga tamkar ba wani abu ba ne illa kawai kawo mutane suna cewa sun ci kaza sun sha kaza. A saboda haka kenan wannan ba abu ne mai mahimmanci ba.

Sai dai ni kuwa ba haka nake kallon abun ba. Ina kallon sa ne daga fannin launin abincin da mafi yawan jama’ar mu ke ci a wannan wata mai tsarki bayan sun kamalla ibadar su da magariba.

Kowa dai ya wuni da azumi, zai so ya yi buda baki da dan abun marmari da kuma ababen gina jiki wadanda zasu mayar da gurbin abunda aka rasa a yayin azumin. Sai dai sauraron irin abunda da mafi yawan al’ummar Hausawa ke shan ruwa da su, abu ne dake kawo hawaye a ido.

“Ni dai yau na sha ruwa da ruwan bunu da rama; yau na ci dabino da kunun kanwa, illa iyaka; ni dai na sha ruwa da dan-wake da mai da yaji, iyakar abunda Allah ya hore min kenan, Allah ya nuna mana gobe lafiya!”

Wadannan sune kadan daga dubban sakonnin da BBC Hausa ke samu a kowanne dare. Me sakonnin suke nuna mana? Lallai suna yin nuni ne da irin wahalar da jama’a suke ciki a kasar mu. Kuma yayinda miliyoyi ke shan “ruwan bunu” wasu ‘yan tsiraru kuwa suna shan kindirmon kwali mai sanyi da naman kaji.

Nigeria dai ba kasa ce matalauciya ba. Amma kuma jam’a na cikin halin matanancin talauci. An san dalilan da suke janyo talaucin: rashin shugabanci na-gari, rashawa, almundahana, rashin adalci da tsananin san-kai. Kididdgar Majalisar Dinkin Duniya na cewa mafi yawan ‘yan Nigeria na rayuwa ne akan kasa da Dala daya – wato kasa da Naira 150 - a rana.

A wannan lokaci na ibada kamata yayi mu kara tunani a game da halayyar mu ko Allah zai ji tausayin mu. Mu gyara halayen mu sannan kuma mu roke Shi Ya ba mu shugabanni masu tausayin talakawa, wadanda zasu fitar da al’ummar mu daga kangin talauci.

A sha ruwa lafiya!

Tuesday, 29 June 2010

Talauci na Janyo Mutuwar Mata Wajen Haihuwa


Da alama matsalar mutuwar mata sanadiyyar haihuwa, na ci gaba da ci wa al'ummar yankin arewacin Nigeria tuwo a kwarya. Kodayake dai wannan ba matsala ce da ta addabi kasar Nigeria kawai ba, a'a sauran kasashe masu tasowa musamman ma a nahiyar Africa su ma suna dimbin hasarar rayukan mata da jira-jirai. Alkaluman hukumar UNICEF na nuna mace daya daga cikin goma sha-uku na mata masu juna biyu kan rasa rayukan su a lokacin haihuwa a nahiyar Afrika.

A wani rahoton BBC, wakilin jihar Jigawa, Muhammad Annur Muhammad, ya bayyana cewa a shekaru ukun da suka shige, alkaluma sun nuna cewa jihar Jigawan ce kan gaba a Nigeria a wannan matsala.

A jihar Borno ma, mata na rasa rayukan su a kullum idan suka zo haihuwa. Duk da bayanan da suke nuna cewa an soma samun nasarar rage matsalar a wasu kasashen tun bayan rattaba hannun kan kudurorin Muradan Majalisar Dinkin Duniya na shekara ta 2015 da shuwagabannin kasashe 147 suka yi, har yanzu akwai jan aiki a gaban Bornon. Lamarin haka yake ma a sauran jihohin arewacin Nigeria. Kodayake dai an tabbatar da cewa shiyyar arewa maso gabashin Najeriyar ce da har yanzu alkaluma ke nuna matsalar tafi ta'azzara.

Amma kuma wasu jihohin arewacin Nigeriar na dan tabusawa. A jihar Jigawa, Mohammed Annur Mohammed na BBC Hausa, ya ce gwamnatin jihar ta shigo da wani shiri wanda ya kunshi horar da al'ummomi musamman na yankunan karkara su kafa wata kungiya da hukumomin ke ilmantar da su bisa hanyoyin kula da mata masu juna biyu, tare da ba su motoci don hanzarta kai matan asibiti.

Akwai matsaloli daban-daban dake janyo mutuwar mata masu juna biyu idan suka zo haihuwa. Babbar matsala dai ita ce talauci. Matan talakawa masu juna biyu sun fi yiwuwar mutuwa idan aka kwatanta da matan mazaje masu hannu da shuni. Saboda rashi, matan talakawa ba sa samun abinci mai gina jiki.

Baya ga wannan, sukan yi ayyuka na karfi, da wahala kamar su noma da surfe da sussuka, har zuwa lokacin da suke gab da zuwa kan-gwiwa. Karfin su kan kare a lokacin da haihuwar ta zo, wanda kuma a lokacin ne suka fi bukatar karfin.

Haka kuma mata marasa ilimi sun fi yiwuwar rasuwa wajen haihuwa fiye da mata masu ilimi saboda sun fi su sanin hanyoyin kaucewa daga wasu haddura; kana sun fi su sanin mahimmancin zuwa asibiti - tun daga lokacin awan ciki har ya zuwa lokacin haihuwa. Alal misali kididdiga ta nuna mata masu ciki biyu cikin goma ne kawai ke zuwa asibiti a jihar Jigawa a yayin da suke da juna biyu.

Matan dake zaune a kauyuka sun fi yiwuwar rasuwa a wajen haihuwa fiye da matan dake zaune a birane. Rashin asibitoci a kauyuka ko kuma nisan da suka yi daga birane na nufin mata masu juna biyu basu cika samun kulawa cikin hanzari a lokacin da suke nakuda ba. So tari kan a je asibiti, sai ka ga rai yayi halin sa. So tari ma har da na jaririn.

Muddin dai yankin Arewacin Nigeria na san cimma manufofin raya kasa, bunkasa da tattalin al'ummar su, ya zama wajibi su tashi haikan wajen tabbatar da daukar matakan da zasu magance wannan matsalar dake janyo hasara mai dimbin yawa ga yankin. Saka idanu wajen kula da jama'a, musamman talakawa babban hakki ne da ya kamata su sauke.

Wednesday, 23 June 2010

Dambe a Majalisar Nigeria: Halin Dattaku?



Hoton dan majalisar wakilan Nigeria kenan Dino Melaye, shugaban kwamitin “Progressive Forum” masu fafutukar kawo sauyi a majalisar wakilan Nigeria. Hotan na nuni da yadda taguwar da yake sanye da ita, ta yage, kana gashi yana sharba gumi. An dai dauki hoton wannan dan majalisar ne bayan damben da aka sha a majalisar wakilan Nigeriar.

Majalisa ta nemi a fitar da ‘yan kungiyar “Progressives” din ne da karfin tuwo bayan sun nemi da a binciki shugaban majalisar wakilan Dimeji Bankole a bisa zargin sama da fadi da kudin jama’a da mulkin kama-karya. Wasu ‘yan majalisar sun fito shabe-shabe yayinda shi kuwa dan majalisa Chinyere Igwe ya samu karaya a hannu bayan wani dan majalisar ya kai masa hari da tukunyar iskar kashe gobara.

Rikici a majalisar dai ya barke ne a jiya (22/06/10) bayan da jim kadan bayan majalisar ta fara zaman ta, kakakinta Bankole ya nemi wani dan majalisa da ya gabatar da moshan (kuduri).

Amma da Mr Melaye ya dago cewa ana kokarin gabatar da moshan din da zai dakatar da ‘yan Progressives” din daga majalisa, sai ya mike, ya fara ihu, yana cewa, “ babu hali, babu hali, ba zamu yadda ba”, yana kuma busa wani usur da ya shiga da shi cikin majalisar.

Kafin a ankara sai wuri ya yamutse, sai naushin juna. An dai yi wannan lamarin ne a gaban ‘yan jarida wadanda kuma suka dauki hotuna da bidiyo. Nan take kuma wasu ‘yan majalisar da jami’an tsaro suka yi kokarin kwace hotunan da ‘yan jarida suka dauka saboda kada duniya ta ga abun kunyar da shugabannin jama’ar suka aikata.

Tuni dai jama’a a ciki da wajen Nigeria suke ta bayyana ra’ayinsu dangane da halayyar mutanen da aka dorawa alhakin yin doka a Nigeria.

A tsakanin kowacce al’umma dake da nutsuwa da sanin ya kamata dai akwai wasu halayya da dabi’u da ya kamata manya su nuna. Mutunta juna, musamman wajen tunkarar mai da martani ga ra’ayin da ya banbanta da na wani na ga kan gaba.

Tsarin democradiyya kuma na jaddada mahimmancin muhawara da bayyana ra’ayi, amma cikin hankali da kwanciyar hankali ba ta hanyar zagi-in-zaga da doke-doke ba.

Dambe da baiwa hammata iska da amfani da makami dan jikkata wani, baya daga cikin halayya ko dabi’un da ake alakantawa da zababbun wakilai masu yiwa kasa doka. Idan kuwa suka yi hakan, lamarin ya kasance mai dokar barci ya bige da gyangyadi kenan. Kuma wabiji ne a hukunta su domin hana faruwar hakan a gaba. Babba, ai misali mai kyau ya kamata ya nunawa na kasa!

Masu sharhi na cewa damben da ya faru a majalisar wakilan Nigeria abun takaici ne. Kuma a cewar su, na nuni da rashin sanin ya kamata da karya mutuncin tsarin democradiyya a Nigeria. Wasu suka ce a daidai wannan lokaci da Nigeria ke kokarin gyara martabar ta a idanun duniya “re-branding”, sai ga manyan jami’an tsarin democradiyya kasar suna kokawa da juna. Tuni dai hotunan wannan abun kunya suka mamaye yanar gizo “internet” inda miliyoyin jama’a suke ta dubawa suna sharhi.

Daga cikin tambayoyin da ake yi yanzu haka har da: shin ‘yan majalisar Nigeriar suna dambe da juna ne saboda kare hakkokin jama’ar da suke wakilta, wadanda kuma talauci da matsayin rayuwa ya addaba, ko kuwa suna baiwa hammata iske ne bisa wasu bukatu na su na kashin kansu?

Sashen Hausa na BBC zai duba wannan batu a wannan makon a shirin sa na “Ra’ayi Riga”.

Wednesday, 28 April 2010

Matasa da Bangar Siyasa a Nigeria


Yanzu haka an fara shiga yanayin siyasa a Nigeria wato yayinda ake shirin gudanar da zabukan shekara mai zuwa.

Siyasa na da mahimmanci a kowacce kasa ta duniya dake bin tarafkin democradiyya. Dalili kuwa shine siyasar tsarin democradiyya na baiwa jama’a damar zabar wanda suke ganin ya dace da su, kuma wanda zai biya masu bukatun su da kuma share masu hawaye.

Jama’a kan ba da goyon baya ga wanda suka yi imanin zai wakilce su – kuma wakilci na gari – ba wanda zai je dan wakiltar kan sa ba. Ta yaya jama’a ya kamata su tabbatar da cewa sun zabi na gari ba zaben tumun dare ba?

Mai yiwuwa sai nan gaba zamu tattauna wannan batu. Amma ina so na yi a wannan sharhi ne akan siyasar banga.

Tun bayan da Nigeria ta koma tsarin democradiyya yau shekaru sama da goma ‘yan siyasar kasar ke amfani da matasa domin cimma manufofin su na siyasa. Ba laifi ba ne ‘yan siyasa su nemi goyon bayan matasa. Misali a baya-bayan nan, kuri’a da goyon bayan matasan Amruka ta taimaka gaya wajen nasarar shugaba Barack Obama a 2008.

Abunda yake laifi shine amfani da matasa a matsayin ‘yan bangar siyasa domin samun nasara a zabe. A zabukan da suka wakana a baya ‘yan siyasa a Nigeria na baiwa matasa kudi, inda su kuma sukan sayi kwaya da sauran ababen sa maye da makamai, suna bi suna razana abokan hamayya da sauran jama’a.

Kamar yadda na gani a wannan hoto dake kan wannan shafi (wanda na dauka sa’ilin da na kai ziyara Bauci a watan jiya), rikici kan rincabe tsakanin ‘yan bangar siyasa. Akan yi fito-na-fito tsakanin ‘yan bangar ‘yan siyasar. Wani lokaci a ji munanan raunuka, a wasu lokuta a rasa rayuka. Wannan abun takaici ne.

Shin matasan nan da suke bari ana amfani da su dan cimma manufar zabe, duk da cewa sun san ‘yan siyasa zasu yi watsi da su, da zarar sun yi nasara, sun san ciwon kan su kuwa? Suna da masaniya kan cewa ‘yan siyasa basu damu da su ba illa kawai sun mai da su tamkar matattakala ce da suke takawa domin “cin zabe” ko ta halin kaka?

Amsar da nake san sani itace: ta yaya ne matasa zasu jajirce su ki yarda ana amfani da su a matsayin ‘yan bangar siyasa a bisa kudi kalilan – wadanda akewa kallon marasa mutunci a Nigeria - lamarin da ka iya sanadiyyar hasarar rayukan su da ci bayan kasar su?

Sunday, 4 April 2010

Facebook | Yaushe Za Su Gane?

Jiki Magayi - Talaka na Mutuwa a Rikice-Rikice


Rikicin addini da na siyasa sune manyan labarun dake janyo fargaba ga Edita ko shugaban kafar yada labarai. Alal misali wajibi ne na tabbatar da cewa mun bada labarin rikice-rikicen addini da kabilancin ba tare da nuna san zuciya ga kowanne bangare ba. Haka ma rikicin siyasa.

Babban abunda na lura da shi a aikina shine a Nigeria kusan kashi casa’in cikin dari na rikice-rikicen da ake yi, manya ne suke ta da su. Manya sun hada da wasu masu kudi, da wasu malaman addini na Musulunci ko Kirista, da wasu ‘yan siyasa.

Tun lokacin da Nigeria ta kama bin hanyar democradiyya a 1999, kasar ta yi fama da rikice-rikicen addini da kabilanci daban daban. Tun daga rikicin OPC Shagamu, Kano, Zangon Kataf, Tibi, Yalwan Shandam har zuwa na baya-bayan nan, wato su Boko Haram, Kala Kato da kuma rikice-rikicen Jos.

Masu bincike sun yi ittifakin cewa manya na da hannu a wadannan rikice-rikice. Suka ce wannan ne ma ya sa aka ki hukunta kowa.

A hirar da na yi da shi a BBC Hausa, tsohon sarkin Gwandu Alhaji Mustapha Jakolo ya yi tambaya mai mahimmanci. Ya ce “kin taba jin wani babban mutum, ko shugaban addini na Musulmi ko na Kirista da aka kashe, ko kuwa ‘ya’yan su? A kullum aka tashi masifa a Nigeria, hasara na tsayawa ne ga talakawan kasar.”

Wannan maganar haka take. Da na je Jos a kwanannan, ilahirin hasara – ta rai da dukiya – ta kare ne kan talaka. Wannan ne ma ya sa ni tambayar: me yasa talakawa ba zasu gano cewa wasu na amfani da su ba ne domin cimma wata manufa? Wani da wahala, wani da riba – shine abunda ke faruwa.

Abunda zan so in ji daga gareku shine: yaushe ne talakan Nigeria zai koyi darasi? Yaushe ne zai daina yarda wasu manya suna amfani da shi, kuma a karshe hasara rai ko ta dan abunda suka mallaka ta komo kansu? Yaushe zai ce, “idan kana so muyi kashe-kashe bamu ‘ya’yan ka mu je tare”?

Lokaci yayi da talaka zai jajirce ya ki karbar ‘yan tsirarun Nairori dan biyan bukatar wasu da a zahiri basu damu da su ba, domin iyalan su na turai su na karatu ko shakatawa da kudaden da ake zargin sun kwashe na su talakawan.

Hausawa dai suka ce jiki magayi.