Saturday 27 February 2010

Banbancin Mutum da Dabba


Da sunan Allah mai Rahama da Jin Kai. Na fara wannan kundi ne da nufin bayyana tunani na, da fahimta ta a game da abubuwan da na ci karo da su a rayuwa.

Shi dai Mahaliccin mu ya bamu kwakwalwa domin yin tunani kuma so tari ina jin ana fada tun ina karama cewa banbancin mutum da dabba shine tunani. A lokacin da nake girma sai nake nazari akan wannan furuci: "banbancin mutum da dabba shine tunani". Hakika haka maganar take.

Sai dai kuma da girma ya zo mani musamman bayan da na fara rayuwa a kasar yammacin duniya inda dabba take da hakki kusan daidai da na bil Adama, sai na fara kallon dabba daga wani bangare. Tun sannan na gano cewa ashe itama dabba tana da tunani kamar mutum. Alal misali ta san mai ba ta abinci, ta san mai korar ta. A sannan ne kuma na fara tunanin cewa mai yiwuwa banbancin mutum da dabba shine: mutum yana iya wasu abubuwa wadanda dabbobi basa yi kamar ikon magana da rubutu da karatu.

Wannan shine arzikin da dan Adam yake da shi: ikon tunani, mu'amala da sauran jama'a, karatu da rubutu, sannan ya hada wadannan hikimomi domin ciyar da rayuwar sa gaba.

Ci gaba shine ginshikin rayuwar mutum. Babu wanda yake san halin "jiya-i-yau". Ko rashin lafiya mutum ke fama da shi yana neman samun sauki, idan Taro kake da shi kana neman ya zama Sisi, idan tumakin ka biyu kana so su zama shidda, idan makota kake shiga debo ruwa to kana san Allah ya hore maka ta yadda zaka haka taka rijiyar a cikin gidan ka, idan a unguwar ku tsibirin shara ya dame ku kana so hukuma ta kirkiro da wani shiri da zai tabbatar da tsaftace muhallin ku...Tambayar anan itace shin kai da ni da kowa na amfani da irin hikimomin da Allah ya hore mana a matsayin mu na bil Adama wajen kawo ci gaba, ba ga rayuwar mu kawai ba, a'a, har ma ta al'ummar mu gabakidaya? A zahiri akwai ayar tambaya.

Mai yiwuwa tunanin ku ya banbanta da nawa...amma ni a ta wa 'yar fahimtar wannan shine tunani dan kalilan na Almajira.

No comments:

Post a Comment