Tuesday 4 January 2011

Mun Shigo 2011 da Tashin Bama-Bamai a Nigeria


Bam ya tashi a Jos! Wannan shine sakon da Bashir Saad Abdullahi ya aiko mani ranar 24 ga watan Disambar 2010.

Wannan harin bam ya tashi ne a wata majami’a ana jaji berin Kirsimeti. Kuma bayan harim bam din na Jos sai aka ci gaba da samun wasu hare-hare ciki harda a Bayelsa da birnin tarayya, Abuja – wato cibiyar gwamnatin Nigeriar.

An dai samu hasarar rayuka da jikkata bayin Allah a wadannan hare-hare. Hare-haren na nuni da mummunan halin rashin tsaron da aka shiga a Nigeria. Gashi kuma lamarin na faruwa a daidai lokaci da kasar ke shirin gudanar da zabuka a duk fadinta a watan Afrilun nan mai zuwa.

Rashin tsaron Nigeria ya samo asali ne sakamakon yin biris da ake zargin jami’an tsaro da shugannin kasa suke yi da harkokin tsaro. Haka kuma ana zargin wasu matsalolin da suka hada da rashin sanin makamar aiki, da san kai a madadin san kasa da kuma tsohuwar matsalar nan dake addabar Nigeria wato cin hanci.

Ko ma dai menene, abunda fashewar bama-baman na makon jiya ke nuni da su shine, Nigeria ta shiga wani sabon babi a fannin rashin tsaro a kasar. Kuma abunda ke faruwa zai kara tsanani muddin dai shugabannin siyasa basu fito sun gudanar da bincike na fisa-bilillahi, kana suka hukunta duk wanda ke da hannu a haddasa tashe-tashen hankula a kasar ba – kana su yi hakan ba sani ba sabo. Muddin ba’a yi haka ba, to za’a yi ta surutu ne ba tare da magance matsalar ba.

Wajibi kuma jama’a su kwarmata duk wani yunkuri da suka ji ana yi na kokarin haddasa masifa a yankunansu. Su tuna cewa: ai idan bam bai fada akanka ba, to idan ya fada kan mahaifinka, ko dan-uwanka tamkar ta fada a kanka ne.

A karshe sai mu ci gaba da yiwa kasar mu addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali domin samun ci gaba.

2 comments:

  1. A gaskiya tashin bama bamai abu ne bako gare mu musamman mu mutanen arewacin Nigeria.
    Amma a zahiri abin na da nasaba da siyasa musamman irin ta kudu maso kudu, Niger delta. Dalili kuwa ai 'yan arewa sun yi gwamnatoci haka kuma 'yan yammaci amma ba a ta samun fashewar bam a wata jaha a arewa in da na sani ba balle abuja da ake tsammatawa matakan tsaro. Allah shi kyauta.

    ReplyDelete
  2. Wata sabuwa kuma. Ashe ba ga bam kadai abin ya tsaya ba.
    Jiya ko kafin dare yayi nisa wasu da ba a san ko su wanene ba suka bude wuta kan wasu mutane suka kashe na kashewa a unguwar federal locost a garin Gombe.
    Abin da ke kulle kai shine dalilin wannan aika aika. Da yawa abinda aka iya ganewa shine wata irin dasisa ta haddasa hargitsi don raba kanun jama'a a kawo siyasar addini don cimma manufa a lokacin da zabe ke kara karatowa. Kuma wannan wata kwangila ce da ake son a baza duk jahohin arewaci.
    Don haka akwai bukatar mabiya addinai su fadaka kuma su fadakar da juna. Allah shi kawo mana sauki kuma ya zaunar da nigeria lafiya.

    ReplyDelete